< Ishaya 2 >
1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
The word that Isaias the son of Amos saw, concerning Juda and Jerusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
And in the last days the mountain of the house of the Lord shall be prepared on the top of mountains, and it shall be exalted above the hills, and all nations shall flow unto it.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
And many people shall go, and say: Come and let us go up to the mountain of the Lord, and to the house of the God of Jacob, and he will teach us his ways, and we will walk in his paths: for the law shall come forth from Sion, and the word of the Lord from Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
And he shall judge the Gentiles, and rebuke many people: and they shall turn their swords into ploughshares, and their spears into sickles: nation shall not lift up sword against nation, neither shall they be exercised any more to war.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
O house of Jacob, come ye, and let us walk in the light of the Lord.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
For thou hast cast off thy people, the house of Jacob: because they are filled as in times past, and have had soothsayers as the Philistines, and have adhered to strange children.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
Their land is filled with silver and gold: and there is no end of their treasures.
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
And their land is filled with horses: and their chariots are innumerable. Their land also is full of idols: they have adored the work of their own hands, which their own fingers have made.
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
And man hath bowed himself down, and man hath been debased: therefore forgive them not.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Enter thou into the rock, and hide thee in the pit from the face of the fear of the Lord, and from the glory of his majesty.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
The lofty eyes of man are humbled, and the haughtiness of men shall be made to stoop: and the Lord alone shall be exalted in that day.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
Because the day of the Lord of hosts shall be upon every one that is proud and highminded, and upon every one that is arrogant, and he shall be humbled.
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
And upon all the tall and lofty cedars of Libanus, and upon all the oaks of Basan.
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
And upon all the high mountains, and upon all the elevated hills.
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
And upon every high tower, and every fenced wall.
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
And upon all the ships of Tharsis, and upon all that is fair to behold.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
And the loftiness of men shall be bowed down, and the haughtiness of men shall be humbled, and the Lord alone shall be exalted in that day.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
And idols shall be utterly destroyed.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And they shall go into the holes of rocks, and into the caves of the earth from the face of the fear of the Lord, and from the glory of his majesty, when he shall rise up to strike the earth.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
In that day a man shall cast away his idols of silver, and his idols of gold, which he had made for himself to adore, moles and bats.
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And he shall go into the clefts of rocks, and into the holes of stones from the face of the fear of the Lord, and from the glory of his majesty, when he shall rise up to strike the earth.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Cease ye therefore from the man, whose breath is in his nostrils, for he is reputed high.