< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
The word that Isaiah the son of Amoz saw concerning Judah and Jerusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
And it shall come to pass in the latter days, that the mountain of Jehovah's house shall be established on the top of the mountains, and shall be exalted above the hills, and all nations shall flow to it.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
And many peoples shall go and say, Come ye, and let us go up to the mountain of Jehovah, to the house of the God of Jacob, and he will teach us of his ways, and we will walk in his paths. For out of Zion shall go forth the law, and the word of Jehovah from Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
And he will judge between the nations, and will decide concerning many peoples, and they shall beat their swords into plowshares, and their spears into pruning-hooks. Nation shall not lift up sword against nation, neither shall they learn war any more.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
O house of Jacob, come ye, and let us walk in the light of Jehovah.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
For thou have forsaken thy people the house of Jacob, because they are filled with things from the east, and are soothsayers like the Philistines. And they strike hands with the children of foreigners.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
And their land is full of silver and gold, neither is there any end of their treasures. Their land is also full of horses, neither is there any end of their chariots.
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
Their land is also full of idols. They worship the work of their own hands, that which their own fingers have made,
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
and so the common man bows down, and the great man degrades himself. Therefore do not forgive them.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Enter into the rock, and hide thee in the dust, from before the terror of Jehovah, and from the glory of his majesty.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
The lofty looks of man shall be brought low, and the haughtiness of men shall be bowed down, and Jehovah alone shall be exalted in that day.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
For there shall be a day of Jehovah of hosts upon all that is proud and haughty, and upon all that is lifted up, and it shall be brought low,
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
and upon all the cedars of Lebanon that are high and lifted up, and upon all the oaks of Bashan,
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
and upon all the high mountains, and upon all the hills that are lifted up,
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
and upon every lofty tower, and upon every fortified wall,
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
and upon all the ships of Tarshish, and upon all pleasant imagery.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
And the loftiness of man shall be bowed down, and the haughtiness of men shall be brought low, and Jehovah alone shall be exalted in that day.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
And the idols shall utterly pass away.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And men shall go into the caves of the rocks, and into the holes of the earth, from before the terror of Jehovah, and from the glory of his majesty, when he arises to shake the earth mightily.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
In that day men shall cast away their idols of silver, and their idols of gold, which have been made for them to worship, to the moles and to the bats,
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
to go into the caverns of the rocks, and into the clefts of the ragged rocks, from before the terror of Jehovah, and from the glory of his majesty, when he arises to shake the earth mightily.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Cease ye from man, whose breath is in his nostrils, for how is he to be accounted of?

< Ishaya 2 >