< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
Detta är tungen öfver Egypti land: Si, Herren skall fara uti enom snarom sky, och komma in uti Egypten; då skola de afgudar uti Egypten bäfva för honom, och de Egyptiers hjerta skall gifva sig i dem.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Och jag skall hetsa, de Egyptier på hvarannan, att en broder skall strida emot den andra, en vän emot den andra, en stad emot den andra, ett rike emot det andra.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
Och de Egyptiers mod skall förgås i dem, och jag skall göra deras anslag omintet; så skola de då fråga deras afgudar och Prester, och spåmän och tecknatydare.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Men jag skall gifva de Egyptier uti grufveliga herrars händer; och en hård Konung skall råda öfver dem, säger den rådandes Herren Zebaoth.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
Och vattnet i hafvet skall uttorkas; dertill skola ock strömmarna, bortsjunka och försvinna.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
Älfverna skola utlöpa, så att dammsjöarna skola förminskas och torre varda; rör och säf förvissna.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
Och gräset vid bäckerna, och all säd vid vattnet skall förfalna, förderfvas och till intet varda.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Och fiskarena skola sörja, och alle de, som fiskakrok kasta i vattnet, skola beklaga sig; och de, som nät utkasta i vattnet, skola bedröfvade varda.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
De skola afgå med skam, som god garn göra, och nät binda.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Och de som fiskakistor hafva, med alla dem som dammar för lön göra, skola ångse varda.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
De Förstar i Zoan äro dårar, Pharaos vise rådgifvare äro i deras råd galne vordne. Hvi sägen I dock om Pharao: Jag är visamannabarn, och är af gamla Konungar kommen?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Hvar äro då nu dine vise? Låt dem förkunna, och undervisa dig, hvad Herren Zebaoth öfver Egypten beslutit hafver.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Men de Förstar i Zoan äro vordne till dårar; de Förstar i Noph äro bedragne; de förföra samt med Egypten hörnstenen för slägten.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
Ty Herren hafver utgjutit en villoanda ibland dem, att de skola förföra Egypten uti allt det de göra, såsom en drucken ragar, då han spyr.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Och Egypten skall ingen hafva, den der för hufvud eller stjert, bål eller gren är.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
På den tiden skall Egypten vara såsom qvinnor, och frukta sig, och förskräckas, då Herren Zebaoth veftar handena öfver dem.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
Och Egypten skall frukta sig för Juda lande, så att den der tänker uppå, han skall förskräckas öfver Herrans Zebaoths råd, som han öfver det beslutit hafver.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
Uti den tiden skola fem städer uti Egypti land tala efter Canaans mål, och svärja vid Herran Zebaoth; en af dem skall heta Irheres.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
På den samma tiden skall Herrans Zebaoths altare vara midt uti Egypti land, och en Herrans vårdsten i gränsone;
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Den ett tecken och vittne vara skall Herranom Zebaoth uti Egypti land; ty de skola ropa till Herran, för sina plågares skull, och han skall sända dem en Frälsare och mästare, som dem hjelpa skall.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Ty Herren skall af, de Egyptier känd varda; och de Egyptier skola känna Herran på den tiden, och skola tjena honom med offer och spisoffer, och skola göra Herranom löfte, och hålla det.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
Och Herren skall slå de Egyptier, och hela dem; ty de skola omvända sig till Herran, och han skall låta bedja sig, och hela dem.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
På den tiden skall en väg vara ifrån Egypten in uti Assyrien, så att de Assyrier skola komma in uti Egypten, och de Egyptier in uti Assyrien, och både Egyptier och Assyrier Gudi tjena.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
På samma tiden skall Israel vara sjelf tredje, med de Egyptier och Assyrier, genom den välsignelse, som på jordene vara skall.
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
Ty Herren Zebaoth skall välsigna dem, och säga: Välsignad äst du Egypten, mitt folk, och du Assur, mina händers verk, och du Israel, mitt arf.

< Ishaya 19 >