< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
La palabra acerca de Egipto. Mira, el Señor está sentado en una nube que se mueve rápidamente y viene a Egipto, y los falsos dioses de Egipto se estremecen con su venida, y el corazón de Egipto se derrite dentro de ellos.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Y enviaré a los egipcios contra los egipcios; y pelearán cada uno contra su hermano, y cada uno contra su prójimo; pueblo contra pueblo, y reino contra reino.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
Y el espíritu de Egipto será desanimado en el, y confundiré sus planes; y se volverán a los dioses falsos, a los brujos, a los que tienen control de los espíritus de los muertos, a los adivinos.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Y entregaré a los egipcios en manos de un amo cruel; y un rey duro será su gobernante, dice el Señor, el Señor de los ejércitos.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
Y las aguas del mar serán cortadas, y el río se secará y se desechará.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
Y los ríos tendrán mal olor. La corriente de Egipto se volverá pequeña y seca: todas las plantas acuáticas quedarán en nada.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
Las tierras de pastoreo junto al Nilo, y todo lo plantado por el Nilo, se secarán, o se quitarán por el viento, y terminarán.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Los pescadores estarán tristes, y todos los que ponen líneas de pesca en el Nilo estarán llenos de pena, y aquellos cuyas redes se extienden sobre las aguas tendrán dolor en sus corazones.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
Y serán decepcionados todos los trabajadores de hilo de lino, y los que hacen tela de algodón.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Y los que hacen redes serán rotas, y los que hacen viveros para peces serán entristecidos.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
Los jefes de Zoan son completamente necios; los guías más sabios de Faraón se han convertido en bestias: ¿cómo le dices a Faraón que soy hijo de los sabios, descendencia de los primeros reyes?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
¿Dónde están tus sabios? Deja que te lo expliquen, que te den conocimiento del propósito del Señor de los ejércitos para Egipto.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Los jefes de Zoán se han vuelto insensatos, los jefes de Menfis, son engañados, los jefes de sus tribus son la causa de que Egipto se haya alejado del camino.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
El Señor ha enviado entre ellos un espíritu de error: y para ellos, Egipto se desvía de la manera correcta en todas sus acciones, ya que un hombre vencido por el vino es incierto en sus pasos.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Y en Egipto no habrá trabajo para ningún hombre, cabeza o cola, alto o bajo, para hacer.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
En ese día, los egipcios serán como mujeres: y la tierra se estremecerá de temor por la agitación de la mano del Señor extendida sobre ella.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
Y la tierra de Judá será causa de gran temor para Egipto; siempre que su nombre venga a la mente, Egipto tendrá miedo ante el Señor de los ejércitos debido a su propósito contra él.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
En ese día habrá cinco pueblos en la tierra de Egipto usando el lenguaje de Canaán y haciendo juramentos al Señor de los ejércitos; y uno de ellos se llamará, La Ciudad de destrucción.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
En aquel día habrá un altar para el Señor en medio de la tierra de Egipto, y una columna para el Señor al borde de la tierra.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Y será una señal y un testimonio para el Señor de los ejércitos en la tierra de Egipto: cuando clamen al Señor contra quien los oprimen, él les enviará un salvador para que los defienda y salve.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Y el Señor se dará a conocer a Egipto, y los egipcios le darán honor al Señor en ese día; Le rendirán culto con ofrendas y ofrendas de comida, y jurarán al Señor y le darán efecto.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
Y el Señor enviará castigo a Egipto, y los herirá; y cuando regresen al Señor, él escuchará su oración y les quitará la enfermedad.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
En ese día habrá una carretera de Egipto a Asiria, y Asiria vendrá a Egipto, y Egipto entrará a Asiria; y los egipcios adorarán al Señor junto con los asirios.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
En ese día, Israel será, junto, con Egipto y Asiria una bendición en medio de la tierra.
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
Por la bendición del Señor de los ejércitos que les ha dado, diciendo: Una bendición para Egipto, mi pueblo, y para Asiria, la obra de mis manos, y para Israel, mi herencia.

< Ishaya 19 >