< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
O fardo do Egito. “Eis que Javé cavalga sobre uma nuvem rápida e vem ao Egito”. Os ídolos do Egito tremerão com sua presença; e o coração do Egito derreterá dentro dele”.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Agitarei os egípcios contra os egípcios, e eles lutarão todos contra seu irmão, e todos contra seu vizinho; cidade contra cidade, e reino contra reino”.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
O espírito dos egípcios falhará dentro deles. Destruirei seus conselhos. Eles buscarão os ídolos, os encantadores, aqueles que têm espíritos familiares e os feiticeiros.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Entregarei os egípcios na mão de um senhor cruel. Um rei feroz governará sobre eles”, diz o Senhor, Yahweh dos Exércitos.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
As águas falharão do mar, e o rio será desperdiçado e ficará seco.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
The os rios se tornarão sujos. Os rios do Egito serão diminuídos e secados. Os canaviais e as bandeiras murcharão.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
Os prados junto ao Nilo, à beira do Nilo, e todos os campos semeados do Nilo, se tornarão secos, serão expulsos e não mais.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Os pescadores lamentarão, e todos aqueles que pescam no Nilo lamentarão, e aqueles que espalham redes sobre as águas definharão.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
Moreover os que trabalham em linho penteado, e os que tecem pano branco, ficarão confusos.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Os pilares serão quebrados em pedaços. Todos aqueles que trabalham por conta de outrem ficarão de luto na alma.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
Os príncipes de Zoan são totalmente insensatos. O conselho dos conselheiros mais sábios do Faraó se tornou estúpido. Como se diz ao Faraó: “Eu sou o filho dos sábios, o filho dos antigos reis”?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Onde estão então seus sábios? Deixe-os dizer-lhe agora; e diga-lhes o que Javé dos exércitos tem proposto em relação ao Egito.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Os príncipes de Zoan se tornaram tolos. Os príncipes de Mênfis estão enganados. Eles fizeram o Egito se desviar, aqueles que são a pedra angular de suas tribos.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
Yahweh misturou um espírito de perversidade no meio dela; e eles fizeram o Egito se desviar em todas as suas obras, como um bêbado cambaleia em seu vômito.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Também não deve haver nenhum trabalho para o Egito, que a cabeça ou a cauda, o ramo da palma ou a pressa, possam fazer.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
Naquele dia, os egípcios serão como as mulheres. Eles tremerão e temerão por causa do tremor da mão de Yahweh dos exércitos, que ele aperta sobre eles.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
A terra de Judá se tornará um terror para o Egito. Todos aqueles a quem for feita menção a ela terão medo, por causa dos planos de Iavé dos Exércitos, que ele determina contra ela.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
Naquele dia, haverá cinco cidades na terra do Egito que falam a língua de Canaã, e juram a Javé de Exércitos. Uma será chamada “A cidade da destruição”.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
Nesse dia, haverá um altar para Iavé no meio da terra do Egito, e um pilar para Iavé em sua fronteira.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Será para um sinal e para uma testemunha a Iavé dos exércitos na terra do Egito; pois eles chorarão a Iavé por causa dos opressores, e ele lhes enviará um salvador e um defensor, e ele os entregará.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Iavé será conhecido pelo Egito, e os egípcios conhecerão Iavé naquele dia. Sim, eles adorarão com sacrifício e oferenda, e farão um voto a Iavé, e o cumprirão.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
Iavé atacará o Egito, atacando e curando. Eles voltarão para Iavé, e ele será tratado por eles, e os curará.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
Nesse dia haverá uma rodovia do Egito para a Assíria, e os assírios entrarão no Egito, e os egípcios na Assíria; e os egípcios adorarão com os assírios.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
Nesse dia, Israel será o terceiro com o Egito e com a Assíria, uma bênção dentro da terra;
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
porque Javé dos Exércitos os abençoou, dizendo: “Bendito seja o Egito meu povo, a Assíria a obra de minhas mãos, e Israel minha herança”.

< Ishaya 19 >