< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
Utsagn om Egypten. Se, Herren farer frem på en lett sky og kommer til Egypten, og Egyptens avguder bever for hans åsyn, og egypternes hjerter smelter i deres indre.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Og jeg vil egge egypter mot egypter, så de skal stride hver mot sin bror og hver mot sin næste, by mot by, rike mot rike.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
Og egypternes ånd skal svikte i deres indre, og deres råd vil jeg gjøre til intet; de skal søke til sine avguder og trollmenn og dødningemanere og sannsigere.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Jeg vil overgi Egypten i en hård herres hånd, og en streng konge skal herske over dem, sier Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
Og vannet i havet blir borte, og elven blir tørr, aldeles uttørret,
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
og elvene stinker, Egyptens strømmer minker og blir tørre; rør og siv visner;
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
engene ved strømmen, ved strømmens bredd, og alt akerland ved strømmen tørker bort, spredes av vinden og er ikke mere.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Fiskerne klager, og alle de som kaster krok i strømmen, sørger, og de som setter garn i vannet, er motløse,
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
og de som arbeider med heklet lin, blir til skamme, og de som vever fint hvitt tøi.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Landets grunnpiller er knust; alle de som arbeider for lønn, er sorgfulle i hu.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
Bare dårer er Soans høvdinger; de viseste blandt Faraos rådgivere gir uforstandige råd. Hvorledes kan I si til Farao: Jeg er en ætling av vismenn, en ætling av fortidens konger?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Hvor er de da dine vismenn, at de kunde forkynne dig, at de kunde forstå hvad råd Herren, hærskarenes Gud, har tatt om Egypten?
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Soans høvdinger er blitt dårer, Nofs høvdinger er blitt narret, og overhodene for stammene har ført Egypten vill.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
Herren har utøst i deres indre en svimmelhets-ånd, og de har ført Egypten vill i all dets gjerning, som en drukken mann forvillet tumler om i sitt spy.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Og ikke skal nogen gjerning lykkes for Egypten, enten det så er hode eller hale, palmegren eller siv som gjør den.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
På den tid skal Egypten være som kvinner; det skal forferdes og frykte for Herrens, hærskarenes Guds løftede hånd, som han svinger imot det.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
Og Juda land skal være en redsel for Egypten; så ofte nogen nevner det for dem, skal de skjelve for det råd som Herren, hærskarenes Gud, tar mot det.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
På den tid skal det være fem byer i Egyptens land som taler Kana'ans tungemål og sverger Herren, hærskarenes Gud, troskap; en av dem skal kalles Ir-Haheres.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
På den tid skal det være et alter for Herren midt i Egyptens land, og en støtte for Herren ved dets landemerke.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Og det skal være til et tegn og et vidne i Egyptens land for Herren, hærskarenes Gud; når de roper til Herren over undertrykkerne, skal han sende dem en frelser og stridsmann og fri dem ut.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Og Herren skal gi sig til kjenne for Egypten, og egypterne skal kjenne Herren på den tid, og de skal bære frem slaktoffer og matoffer og gjøre løfter til Herren og holde dem.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
Herren skal slå Egypten, han skal slå, men også læge, og de skal vende om til Herren, og han skal bønnhøre dem og læge dem.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
På den tid skal det være en ryddet vei fra Egypten til Assyria, og assyrerne skal komme til Egypten, og egypterne til Assyria, og egypterne skal tjene Herren sammen med assyrerne.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
På den tid skal Israel være den tredje med Egypten og med Assyria, en velsignelse midt på jorden,
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
fordi Herren, hærskarenes Gud, har velsignet det og sagt: Velsignet være mitt folk Egypten og mine henders verk Assyria og min arv Israel!

< Ishaya 19 >