< Ishaya 19 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
Weissagung über Ägypten. Siehe, Jehovah fährt daher auf leichter Wolke und kommt nach Ägypten, und Ägyptens Götzen erbeben vor Seinem Angesicht, und Ägyptens Herz zerschmilzt in seinem Inneren.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Und Ich will Ägypter wider Ägypter verwirren, daß sie streiten, der Mann gegen seinen Bruder, und ein Mann gegen seinen Genossen, Stadt gegen Stadt, Königreich wider Königreich.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
Und ausgeleert soll werden der Geist Ägyptens in seinem Inneren, und seinen Rat will Ich verschlingen. Und sie werden die Götzen befragen und die Bezauberer und die Totenbeschwörer und die Zeichendeuter.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Und Ich überantworte die Ägypter in die Hand eines harten Herrn, und ein starker König soll herrschen über sie, spricht der Herr Jehovah der Heerscharen.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
Und versiegen sollen die Wasser aus dem Meer, und der Fluß soll austrocknen und trocken werden.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
Und die Flüsse werden verlaufen, arm und ausgetrocknet werden die Ströme Ägyptens; Rohr und Schilf versiechen.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
Und die Auen am Strom und an der Mündung des Stromes, und alle Saat des Stromes verdorrt, zerstiebt und ist nicht mehr.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Und die Fischer ächzen und es trauern alle, so die Angel werfen in den Strom; und die, so das Fischernetz ausbreiten über der Wasser Fläche, verschmachten.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
Beschämt werden die, so in Seidenflachs arbeiten, und die weben durchbrochenes Zeug.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Zerstoßen sind seine Grundpfeiler; alle, die um den Lohn Teiche für Fische machen.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
Nur Narren sind die Obersten Zoans, die Weisen der Räte Pharaos, ihr Rat ist unvernünftig geworden. Wie sprechet ihr zu Pharao: Ein Sohn der Weisen bin ich, ein Sohn von Königen der Vorzeit.
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Wo sind sie nun, deine Weisen? Und laß doch sie dir ansagen und wissen, was Jehovah der Heerscharen über Ägypten hat beratschlagt?
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Närrisch sind Zoans Oberste, verführt die Obersten Nophs, sie führen Ägypten, den Eckstein seiner Stämme, irre.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
Jehovah goß den Geist der Verkehrtheiten in sein Inneres, daß sie Ägypten in all seinem Tun irre führen, wie in seinem Gespei der Trunkene irre geht.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Kein Werk hat Ägypten, das Kopf und Schwanz, Palmast und Binse ausmachte.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
An jenem Tage wird Ägypten sein wie Weiber, und wird erzittern und schaudern vor dem Schwingen der Hand Jehovahs der Heerscharen, wenn Er sie schwingt über sie.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
Und Jehudahs Boden wird für Ägypten ein Schreckwort. Jeder, der sein gedenkt bei ihm, schaudert vor dem Ratschluß Jehovahs der Heerscharen, den Er gegen es beschlossen.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
An jenem Tage werden in Ägyptenland fünf Städte sein, so reden mit der Lippe Kanaans und schwören bei Jehovah der Heerscharen. Sonnenstadt heißt man die eine.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
An jenem Tag wird ein Altar für Jehovah sein in der Mitte des Landes Ägypten und neben seiner Grenze eine Denksäule für Jehovah.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Und wird zum Zeichen und zum Zeugnis für Jehovah der Heerscharen im Land Ägypten. Wenn sie schreien zu Jehovah ob den Unterdrückern, wird Er ihnen einen Retter und Fürsten senden, daß Er sie errette.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Und kund wird den Ägyptern Jehovah werden, daß an jenem Tage die Ägypter Jehovah kennen und Ihm mit Schlachtopfer und Speiseopfer dienen, und Gelübde Jehovah geloben und entrichten.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
Und Jehovah wird Ägypten schlagen, es schlagen und heilen, und sie werden zu Jehovah zurückkehren, und Er läßt Sich von ihnen erflehen und heilt sie.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
An jenem Tag wird eine Bahn von Ägypten nach Aschur sein, und Aschur nach Ägypten und Ägypten nach Aschur kommen; und die Ägypter werden Aschur dienen.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
An jenem Tag wird Israel der dritte sein für Ägypten und für Aschur, ein Segen inmitten des Landes,
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
Das segnen wird Jehovah der Heerscharen und sprechen: Gesegnet sei Mein Volk Ägypten und Aschur, Meiner Hände Werk, und Israel, Mein Erbe.