< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
Malheur accablant de l’Egypte. Voici que le Seigneur montera sur un nuage léger, et qu’il entrera dans l’Egypte, et que seront ébranlés les simulacres de l’Egypte devant sa face, et le cœur de l’Egypte se fondra au milieu d’elle.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Et je ferai courir des Egyptiens contre des Egyptiens; et un homme combattra contre son frère, et un homme contre un ami, une cité contre une cité, un royaume contre un royaume.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
Et l’esprit de l’Egypte sera déchiré dans ses entrailles, et je détruirai son conseil; et ils interrogeront leurs simulacres, et leurs devins, et les pythoniens et les magiciens.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Et je livrerai l’Egypte à la main de maîtres cruels, et un roi puissant les dominera, dit le Seigneur Dieu des armées.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
Et l’eau disparaîtra de la mer, et le fleuve sera détruit et desséché.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
Et les rivières tariront, et les ruisseaux, retenus par des digues, diminueront et seront desséchés. Le roseau et le jonc se flétriront;
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
Le lit du ruisseau sera mis à nu à sa source même, et l’eau dont on arrosait toute semence desséchera, deviendra aride, et ne sera plus.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Et les pêcheurs s’affligeront, et tous ceux qui jettent l’hameçon dans le fleuve pleureront, et ceux qui tendent le filet sur la surface des eaux dépériront.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
Ils seront confondus, ceux qui travaillaient le lin, qui le cardaient et en faisaient de fins tissus.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Et ses lieux arrosés d’eau se dessécheront, de même tous ceux qui faisaient des fosses pour prendre des poissons.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
Ils sont atteints de folie, les princes de Tanis, les sages conseillers de Pharaon ont donné un conseil insensé. Comment direz-vous à Pharaon: Je suis fils des sages, fils des anciens rois?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Où sont maintenant tes sages? Qu’ils t’annoncent, qu’ils apprennent ce qu’a résolu le Seigneur des armées, touchant l’Egypte.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Ils sont devenus fous, les princes de Tanis; ils se sont amoindris, les princes de Memphis, ils ont séduit l’Egypte, soutien de ses peuples.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
Le Seigneur a répandu au milieu d’elle un esprit de vertige, et ils ont fait errer l’Egypte dans toutes ses œuvres, comme erre l’homme ivre et qui vomit.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Et il n’y aura pour l’Egypte rien à faire à la tête et à la queue, à celui qui plie et à celui qui refrène.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
Et ce jour-là, les Egyptiens seront comme des femmes, et ils s’étonneront, et ils craindront à la vue de la commotion que la main du Seigneur des armées lui-même produira sur eux.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
Et la terre de Juda sera à l’Égypte en effroi; quiconque s’en souviendra sera effrayé à la vue du dessein que le Seigneur des armées lui-même a formé contre elle.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
En ce jour-là, il y aura cinq cités dans la terre d’Égypte qui parleront la langue de Chanaan, et qui jureront par le Seigneur des armées; l’une sera appelée la cité du soleil.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
En ce jour-là, il y aura un autel du Seigneur au milieu de la terre d’Égypte, et un monument au Seigneur près de sa frontière.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Ce sera en signe et en témoignage au Seigneur des armées dans la terre d’Égypte. Car ils crieront vers le Seigneur à la vue de l’oppresseur, et il leur enverra un sauveur et un défenseur, qui les délivrera.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Et le Seigneur sera connu de l’Égypte, et les Égyptiens en ce jour-là connaîtront le Seigneur; et ils l’honoreront par des hosties et par des offrandes; et ils voueront des vœux et ils les acquitteront.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
Et le Seigneur frappera l’Égypte d’une plaie, et il la guérira; et il s’apaisera pour eux et il les guérira.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
En ce jour-là, il y aura une voie de l’Égypte chez les Assyriens, et l’Assyrien entrera dans l’Égypte, et l’Égyptien chez les Assyriens, et les Égyptiens serviront Assur.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
En ce jour-là, Israël sera réuni comme troisième à l’Égyptien et à l’Assyrien; la bénédiction sera au milieu de la terre,
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
Qu’a bénie le Seigneur des armées, disant: Béni soit mon peuple d’Égypte, et l’ouvrage de mes mains se fera par l’Assyrien, mais mon héritage est Israël.

< Ishaya 19 >