< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
La charge de l'Egypte. Voici, l'Eternel s'en va monter sur une nuée légère, et il entrera dans l'Egypte; et les idoles d'Egypte s'enfuiront de toutes parts de devant sa face, et le cœur de l'Egypte se fondra au milieu d'elle.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
Et je ferai venir pêle-mêle l'Egyptien contre l'Egyptien, et chacun fera la guerre contre son frère, et chacun contre son ami, ville contre ville, Royaume contre Royaume.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
L'esprit de l'Egypte s'évanouira au milieu d'elle, et je dissiperai son conseil, et ils interrogeront les idoles, et les enchanteurs, et les esprits de Python, et les diseurs de bonne aventure.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
Et je livrerai l'Egypte en la main d'un Seigneur sévère, et un Roi cruel dominera sur eux, dit le Seigneur, l'Eternel des armées.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
Et les eaux de la mer défaudront, et le fleuve séchera, et tarira.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
Et on fera détourner les fleuves; les ruisseaux des digues s'abaisseront et sécheront; les roseaux et les joncs seront coupés.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
Les prairies qui sont près des ruisseaux, et sur l'embouchure du fleuve, et tout ce qui aura été semé le long des ruisseaux, séchera, sera jeté loin, et ne sera plus.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
Et les pêcheurs gémiront, et tous ceux qui jettent l'hameçon au fleuve, mèneront deuil, et ceux qui étendent les rets sur les eaux, languiront.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
Ceux qui travaillent en lin et en fin crêpe, et ceux qui tissent les filets, seront honteux.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
Et ses chaussées seront rompues; et tous ceux qui font des écluses de viviers seront contristés de cœur.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
Certes les principaux de Tsohan sont fous, les sages d'entre les conseillers de Pharaon sont un conseil abruti; comment dites-vous à Pharaon; je suis fils des sages, le fils des Rois anciens?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Où sont-ils maintenant? où sont, [dis-je], tes sages? qu'ils t'annoncent, je te prie, s'ils le savent, ce que l'Eternel des armées a décrété contre l'Egypte.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
Les principaux de Tsohan sont devenus insensés; les principaux de Noph se sont trompés; les Cantons des Tribus d'Egypte l'ont fait égarer.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
L'Eternel a versé au milieu d'elle un esprit de renversement, et on a fait errer l'Egypte dans toutes ses œuvres, comme un homme ivre se vautre dans son vomissement.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Et il n'y aura aucun ouvrage qui serve à l'Egypte, [rien de ce] que fera la tête ou la queue, le rameau ou le jonc.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
En ce jour-là l'Egypte sera comme des femmes, et elle sera étonnée et épouvantée à cause de la main élevée de l'Eternel des armées, laquelle il s'en va élever contr'elle.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
Et la terre de Juda sera en effroi à l'Egypte; quiconque fera mention d'elle, en sera épouvanté en soi-même, à cause du conseil de l'Eternel des armées, lequel il s'en va décréter contr'elle.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
En ce jour-là il y aura cinq villes au pays d'Egypte qui parleront le langage de Chanaan, et qui jureront à l'Eternel des armées; et l'une sera appelée Ville de destruction.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
En ce jour-là il y aura un autel à l'Eternel au milieu du pays d'Egypte, et une enseigne dressée à l'Eternel sur sa frontière.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
Et [cela] sera pour signe et pour témoignage à l'Eternel des armées dans le pays d'Egypte; car ils crieront à l'Eternel à cause des oppresseurs, et il leur enverra un libérateur, et un grand personnage qui les délivrera.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
Et l'Eternel se fera connaître à l'Egypte; et en ce jour-là l'Egypte connaîtra l'Eternel, et le servira, offrant des sacrifices et des gâteaux, et elle vouera des vœux à l'Eternel, et les accomplira.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
L'Eternel donc frappera les Egyptiens, les frappant et les guérissant, et ils retourneront jusques à l'Eternel, qui sera fléchi par leurs prières, et les guérira.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
En ce jour-là il y aura un chemin battu de l'Egypte en Assyrie; et l'Assyrie viendra en Egypte, et l'Egypte en Assyrie, et l'Egypte servira avec l'Assyrie.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
En ce jour-là Israël sera [joint] pour [la] troisième [partie] à l'Egypte et à l'Assyrie, et la bénédiction sera au milieu de la terre.
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
Ce que l'Eternel des armées bénira, en disant: Bénie soit l'Egypte mon peuple; et [bénie soit] l'Assyrie l'ouvrage de mes mains; et Israël mon héritage.

< Ishaya 19 >