< Ishaya 19 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
The word about Egypt. See, the Lord is seated on a quick-moving cloud, and is coming to Egypt: and the false gods of Egypt will be troubled at his coming, and the heart of Egypt will be turned to water.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
And I will send the Egyptians against the Egyptians: and they will be fighting every one against his brother, and every one against his neighbour; town against town, and kingdom against kingdom.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
And the spirit of Egypt will be troubled in her, and I will make her decisions without effect: and they will be turning to the false gods, and to those who make hollow sounds, and to those who have control of spirits, and to those who are wise in secret arts.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
And I will give the Egyptians into the hand of a cruel lord; and a hard king will be their ruler, says the Lord, the Lord of armies.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
And the waters of the sea will be cut off, and the river will become dry and waste:
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
And the rivers will have an evil smell; the stream of Egypt will become small and dry: all the water-plants will come to nothing.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
The grass-lands by the Nile, and everything planted by the Nile, will become dry, or taken away by the wind, and will come to an end.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
The fishermen will be sad, and all those who put fishing-lines into the Nile will be full of grief, and those whose nets are stretched out on the waters will have sorrow in their hearts.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
And all the workers in linen thread, and those who make cotton cloth, will be put to shame.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
And the makers of twisted thread will be crushed, and those who ... will be sad in heart.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
The chiefs of Zoan are completely foolish; the wisest guides of Pharaoh have become like beasts: how do you say to Pharaoh, I am the son of the wise, the offspring of early kings?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Where, then, are your wise men? let them make clear to you, let them give you knowledge of the purpose of the Lord of armies for Egypt.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
The chiefs of Zoan have become foolish, the chiefs of Noph are tricked, the heads of her tribes are the cause of Egypt's wandering out of the way.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
The Lord has sent among them a spirit of error: and by them Egypt is turned out of the right way in all her doings, as a man overcome by wine is uncertain in his steps.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
And in Egypt there will be no work for any man, head or tail, high or low, to do.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
In that day the Egyptians will be like women: and the land will be shaking with fear because of the waving of the Lord's hand stretched out over it.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
And the land of Judah will become a cause of great fear to Egypt; whenever its name comes to mind, Egypt will be in fear before the Lord of armies because of his purpose against it.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
In that day there will be five towns in the land of Egypt using the language of Canaan, and making oaths to the Lord of armies; and one of them will be named, The Town of the Sun.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
In that day there will be an altar to the Lord in the middle of the land of Egypt, and a pillar to the Lord at the edge of the land.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
And it will be a sign and a witness to the Lord of armies in the land of Egypt: when they are crying out to the Lord because of their cruel masters, then he will send them a saviour and a strong one to make them free.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
And the Lord will give the knowledge of himself to Egypt, and the Egyptians will give honour to the Lord in that day; they will give him worship with offerings and meal offerings, and will take an oath to the Lord and give effect to it.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
And the Lord will send punishment on Egypt, and will make them well again; and when they come back to the Lord he will give ear to their prayer and take away their disease.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
In that day there will be a highway out of Egypt to Assyria, and Assyria will come into Egypt, and Egypt will come into Assyria; and the Egyptians will give worship to the Lord together with the Assyrians.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
In that day Israel will be the third together with Egypt and Assyria, a blessing in the earth:
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
Because of the blessing of the Lord of armies which he has given them, saying, A blessing on Egypt my people, and on Assyria the work of my hands, and on Israel my heritage.

< Ishaya 19 >