< Ishaya 19 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
The burden of Egypt. Behold, Jehovah rides upon a swift cloud, and comes to Egypt. And the idols of Egypt shall tremble at his presence, and the heart of Egypt shall melt in the midst of it.
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
And I will stir up the Egyptians against the Egyptians, and they shall fight each one against his brother, and each one against his neighbor, city against city, kingdom against kingdom.
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
And the spirit of Egypt shall fail in the midst of it, and I will destroy the counsel of it. And they shall seek for the idols, and for the charmers, and for those who have familiar spirits, and for the wizards.
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
And I will give over the Egyptians into the hand of a cruel lord. And a fierce king shall rule over them, says the Lord, Jehovah of hosts.
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
And the waters shall fail from the sea, and the river shall be wasted and become dry.
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
And the rivers shall become foul. The streams of Egypt shall be diminished and dried up. The reeds and flags shall wither away.
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
The meadows by the Nile, by the brink of the Nile, and all the sown fields of the Nile, shall become dry, be driven away, and be no more.
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
And the fishermen shall lament, and all those who cast a hook into the Nile shall mourn, and those who spread nets upon the waters shall languish.
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
Moreover those who work in combed flax, and those who weave white cloth, shall be confounded.
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
And the pillars of Egypt shall be broken in pieces. All those who work for hire shall be grieved in soul.
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
The rulers of Zoan are utterly foolish. The counsel of the wisest counselors of Pharaoh has become brutish. How will ye say to Pharaoh, I am the son of wise men, the son of ancient kings?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
Where then are thy wise men? And let them tell thee now, and let them know what Jehovah of hosts has purposed concerning Egypt.
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
The rulers of Zoan have become fools. The rulers of Memphis are deceived. They have caused Egypt to go astray, the chief of her tribes.
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
Jehovah has mingled a spirit of perverseness in the midst of her, and they have caused Egypt to go astray in every work of it, as a drunken man staggers in his vomit.
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
Neither shall there be for Egypt any work, which head or tail, palm-branch or rush, may do.
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
In that day the Egyptians shall be like women, and they shall tremble and fear because of the shaking of the hand of Jehovah of hosts, which he shakes over them.
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
And the land of Judah shall become a terror to Egypt. Everyone to whom mention is made of it shall be afraid because of the purpose of Jehovah of hosts, which he purposes against it.
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
In that day there shall be five cities in the land of Egypt that speak the language of Canaan, and swear to Jehovah of hosts. One shall be called The city of destruction.
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
In that day shall there be an altar to Jehovah in the midst of the land of Egypt, and a pillar to Jehovah at the border of it.
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
And it shall be for a sign and for a witness to Jehovah of hosts in the land of Egypt. For they shall cry to Jehovah because of oppressors, and he will send them a savior, and a defender, and he will deliver them.
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
And Jehovah shall be known to Egypt, and the Egyptians shall know Jehovah in that day. Yea, they shall worship with sacrifice and oblation, and shall vow a vow to Jehovah, and shall perform it.
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
And Jehovah will smite Egypt, smiting and healing, and they shall return to Jehovah. And he will be entreated by them, and will heal them.
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
In that day there shall be a highway out of Egypt to Assyria. And the Assyrian shall come into Egypt, and the Egyptian into Assyria, and the Egyptians shall worship with the Assyrians.
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
In that day Israel shall be the third with Egypt and with Assyria, a blessing in the midst of the earth,
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
in that Jehovah of hosts has blessed them, saying, Blessed be Egypt my people, and Assyria the work of my hands, and Israel my inheritance.