< Ishaya 18 >

1 Kaiton ƙasar da ake jin ƙarar fikafikai a bakin kogunan Kush,
Ho! Terre aux navires ailés qui es au delà des fleuves d'Ethiopie,
2 wadda ta aiko da jakadu ta teku cikin jiragen ruwan da aka yi da kyauro a bisa ruwa. Ku tafi, ku’yan saƙo masu sauri, zuwa ga dogayen mutane masu sulɓin jiki, zuwa ga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko tana jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba.
toi qui envoies des messagers sur la mer dans des nefs de roseau sur la surface des eaux! Allez, émissaires légers, vers la nation robuste et agile, vers le peuple dès son origine et toujours formidable, nation qui nivelle et écrase, dont des fleuves coupent le pays!
3 Ku dukan mutanen duniya, ku da kuke zama a duniya, sa’ad da aka ɗaga tutar a kan duwatsu, za ku gan shi, sa’ad da kuma aka busa ƙaho, za ku ji shi.
Vous tous, habitants du monde et habitants de la terre, quand on dressera l'étendard sur les montagnes, regardez! et quand on sonnera de la trompette, écoutez!
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Zan yi shiru in kuma duba a hankali daga mazaunina, kamar ƙuna mai zafi a hasken rana, kamar girgijen raba a lokacin girbi.”
Car, ainsi me parle l'Éternel: Tranquille, je regarde de ma demeure, pendant la chaleur sereine aux rayons du soleil, et à la vapeur de rosée durant la chaleur de la moisson.
5 Gama kafin girbi, sa’ad da furanni suka karkaɗe furanni kuma suka zama’ya’yan inabin da suka nuna, zai faffalle rassan kuringar inabi da wuƙa, ya yanke ya kuma kwashe rassan da suka bazu.
Car avant la moisson, quand la crue sera complète, et que la fleur aura passé en raisin mûr, alors il tranchera les sarments avec la serpe, et enlèvera les pampres, et les coupera.
6 Duk za a bar su wa tsuntsayen dutse su ci da kuma namun jeji; tsuntsaye kuma za su ci rani a kansu, namun jeji kuma za su yi damina a kansu.
Ils seront tous livrés aux oiseaux de proie des montagnes et aux bêtes des champs, et les oiseaux de proie y passeront un été, et toutes les bêtes des champs un hiver.
7 A wannan lokaci za a kawo kyautai wa Ubangiji Maɗaukaki daga dogayen mutane masu sulɓin jiki, daga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko na jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba. Za a kawo kyautai zuwa Dutsen Sihiyona, wurin da Sunan Ubangiji Maɗaukaki yake.
En ce même temps, des offrandes seront apportées à l'Éternel des armées par le peuple robuste et agile, et par le peuple dès son origine et toujours formidable, nation qui nivelle et écrase, dont des fleuves coupent le pays, dans la résidence de l'Éternel des armées, sur la montagne de Sion.

< Ishaya 18 >