< Ishaya 18 >

1 Kaiton ƙasar da ake jin ƙarar fikafikai a bakin kogunan Kush,
Ah, the land of the rustling of wings, which is beyond the rivers of Ethiopia,
2 wadda ta aiko da jakadu ta teku cikin jiragen ruwan da aka yi da kyauro a bisa ruwa. Ku tafi, ku’yan saƙo masu sauri, zuwa ga dogayen mutane masu sulɓin jiki, zuwa ga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko tana jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba.
that sends ambassadors by the sea, even in vessels of papyrus upon the waters, saying, Go, ye swift messengers, to a nation tall and smooth, to a people fearful from their beginning onward, a nation that metes out and treads down, whose land the rivers divide!
3 Ku dukan mutanen duniya, ku da kuke zama a duniya, sa’ad da aka ɗaga tutar a kan duwatsu, za ku gan shi, sa’ad da kuma aka busa ƙaho, za ku ji shi.
All ye inhabitants of the world, and ye dwellers on the earth, when an ensign is lifted up on the mountains, see ye, and when the trumpet is blown, hear ye.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Zan yi shiru in kuma duba a hankali daga mazaunina, kamar ƙuna mai zafi a hasken rana, kamar girgijen raba a lokacin girbi.”
For thus Jehovah has said to me, I will be still, and I will behold in my dwelling-place, like clear heat in sunshine, like a cloud of dew in the heat of harvest.
5 Gama kafin girbi, sa’ad da furanni suka karkaɗe furanni kuma suka zama’ya’yan inabin da suka nuna, zai faffalle rassan kuringar inabi da wuƙa, ya yanke ya kuma kwashe rassan da suka bazu.
For before the harvest, when the blossom is over, and the flower becomes a ripening grape, he will cut off the sprigs with pruning-hooks, and he will take away and cut down the spreading branches.
6 Duk za a bar su wa tsuntsayen dutse su ci da kuma namun jeji; tsuntsaye kuma za su ci rani a kansu, namun jeji kuma za su yi damina a kansu.
They shall be left together to the ravenous birds of the mountains, and to the beasts of the earth. And the ravenous birds shall summer upon them, and all the beasts of the earth shall winter upon them.
7 A wannan lokaci za a kawo kyautai wa Ubangiji Maɗaukaki daga dogayen mutane masu sulɓin jiki, daga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko na jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba. Za a kawo kyautai zuwa Dutsen Sihiyona, wurin da Sunan Ubangiji Maɗaukaki yake.
In that time a present shall be brought to Jehovah of hosts from a people tall and smooth, even from a people fearful from their beginning onward, a nation that metes out and treads down, whose land the rivers divide, to the place of the name of Jehovah of hosts, the mount Zion.

< Ishaya 18 >