< Ishaya 17 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Damaskus. “Duba, Damaskus ba za tă ƙara zama birni ba amma za tă zama tsibin juji.
Şam'la ilgili bildiri: İşte Şam kent olmaktan çıkacak, Enkaz yığınına dönecek.
2 Za a watse a bar biranen Arower a bar wa tumaki da shanu, waɗanda za su kwanta, ba tare da wani wanda zai tsorata su ba.
Aroer kentleri terk edilecek, Hayvan sürüleri orada yatacak, Onları ürküten olmayacak.
3 Birni mai katanga za tă ɓace daga Efraim, ikon sarauta kuma daga Damaskus; raguwar Aram za tă zama kamar darajar Isra’ila,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Efrayim'de surlu kent kalmayacak, Şam'ın egemenliği yok olacak. Sağ kalan Aramlılar'ın onuru İsrail'in onuru gibi kırılacak. Her Şeye Egemen RAB böyle diyor.
4 “A wannan rana ɗaukakar Yaƙub za tă ƙare; kitsen jikinsa zai lalace.
O gün Yakup soyunun görkemi sönecek, Hepsi bir deri bir kemik kalacak.
5 Zai zama kamar sa’ad da mai girbi ya tara hatsin da yake tsaye ya kuma girbe hatsin da hannunsa kamar sa’ad da mutum ya yi kala kawunan hatsi a Kwarin Refayim.
İsrail, ekinin elle biçilip Başakların devşirildiği bir tarla, Refaim Vadisi'nde hasattan sonra Başakların toplandığı bir tarla gibi olacak.
6 Duk da haka waɗansu kala za su ragu, sai ka ce sa’ad da an karkaɗe itace zaitun, aka bar’ya’yan zaitun biyu ko uku a can ƙwanƙolin rassan, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassa na gefe na itace mai’ya’ya,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Çok az kişi kurtulacak. Artakalanların sayısı, dövüldükten sonra tepesinde iki üç, Dal uçlarında dört beş zeytin tanesi kalan Zeytin ağacı gibi olacak. İsrail'in Tanrısı RAB böyle diyor.
7 A wannan rana mutane za su nemi Mahaliccinsu su kuma juye idanunsu ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
O gün insanlar kendilerini yaratana bakacaklar, gözleri İsrail'in Kutsalı'nı görecek.
8 Ba za su dubi bagade ba, waɗanda suke aikin hannuwansu, ba za su kuma kula da ginshiƙan Ashera ba da kuma bagadan turaren da yatsotsinsu suka yi.
Elleriyle yaptıkları sunaklara, parmaklarıyla biçim verdikleri Aşera putlarına, buhur sunaklarına bakmayacaklar.
9 A wannan rana biranensu masu ƙarfi, waɗanda suka bari saboda Isra’ilawa, za su zama kamar wuraren da aka ƙyale suka zama kufai a jeji. Za su kuma zama kango.
O gün İsrail'in güçlü kentleri İsrailliler'den kaçan Amorlular'la Hivliler'in Terk ettiği kentler gibi ıssız olacak.
10 Kun manta da Allah Mai Cetonku; ba ku tuna da Dutse, kagararku ba. Saboda haka, ko da yake kun fita ku shuka tsire-tsire mafi kyau kuka kuma shuka inabin da aka sayo daga waje,
Çünkü, ey İsrail, seni kurtaran Tanrı'yı unuttun, Sığındığın Kaya'yı anmaz oldun. Bunun yerine, güzel fidanlar, ithal asmalar dikiyorsun.
11 ko da yake a ranar kun shuka su, kuka sa su yi girma, da safe kuma sa’ad da kuka shuka su, kuka sa suka yi toho suka yi fure, duk da haka girbin ba zai zama kome ba a ranar cuta da zafin da ba ta da magani.
Onlar diktiğin gün filizlenip Ertesi sabah tomurcuklanabilir. Ama hastalık ve dinmez acı gününde meyve vermeyecekler.
12 Kash, ga hayaniyar al’ummai masu yawa suna hayaniya kamar rurin teku! Kash, ga fushin mutane suna ruri kamar rugugi kamar manyan ruwaye!
Eyvah, çok sayıda ulus kükrüyor, Azgın deniz gibi gürlüyorlar. Halklar güçlü sular gibi çağlıyor.
13 Ko da yake mutane suna ruri kamar sukuwar raƙuman ruwa, sa’ad da ya tsawata musu za su gudu can da nisa, aka kore su kamar yayinda iska ya hura a kan tuddai, kamar tattake kuma a cikin guguwa.
Halklar kabaran sular gibi çağlayabilir, Ama Tanrı onları azarlayınca uzaklara kaçacaklar. Rüzgarın önünde dağdaki saman ufağı gibi, Kasırganın önünde diken yumağı gibi savrulacaklar.
14 Da yamma, sai razana ba tsammani! Kafin safiya, duk sun ɓace! Wannan ne rabon waɗanda suka washe mu, rabon waɗanda suka yi mana ƙwace.
Akşam dehşet saçıyorlardı, Sabah olmadan yok olup gittiler. Bizi yağmalayanların, bizi soyanların sonu budur.

< Ishaya 17 >