< Ishaya 17 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Damaskus. “Duba, Damaskus ba za tă ƙara zama birni ba amma za tă zama tsibin juji.
این است پیغام خدا دربارهٔ دمشق: «دمشق از بین خواهد رفت و تبدیل به ویرانه خواهد شد.
2 Za a watse a bar biranen Arower a bar wa tumaki da shanu, waɗanda za su kwanta, ba tare da wani wanda zai tsorata su ba.
شهرهای”عروعیر“متروک خواهند شد و گوسفندان در آنجا خواهند خوابید و کسی نخواهد بود که آنها را بترساند.
3 Birni mai katanga za tă ɓace daga Efraim, ikon sarauta kuma daga Damaskus; raguwar Aram za tă zama kamar darajar Isra’ila,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
اسرائیل قدرتش را از دست خواهد داد و دمشق سقوط خواهد کرد. بازماندگان سوریه مانند قوم اسرائیل خوار و ضعیف خواهند شد.» این را خداوند لشکرهای آسمان فرموده است.
4 “A wannan rana ɗaukakar Yaƙub za tă ƙare; kitsen jikinsa zai lalace.
خداوند می‌فرماید: «عظمت اسرائیل محو خواهد شد و ثروتش از بین خواهد رفت.
5 Zai zama kamar sa’ad da mai girbi ya tara hatsin da yake tsaye ya kuma girbe hatsin da hannunsa kamar sa’ad da mutum ya yi kala kawunan hatsi a Kwarin Refayim.
در آن روز، اسرائیل مانند کشتزارهای درهٔ رفائیم خواهد بود که پس از درو، چیزی در آن باقی نمی‌ماند.
6 Duk da haka waɗansu kala za su ragu, sai ka ce sa’ad da an karkaɗe itace zaitun, aka bar’ya’yan zaitun biyu ko uku a can ƙwanƙolin rassan, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassa na gefe na itace mai’ya’ya,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila.
عدهٔ بسیار کمی از قوم اسرائیل باقی خواهند ماند، همان‌گونه که پس از چیدن زیتون دو سه دانه روی شاخه‌های بلند، و چهار پنج دانه نوک شاخه‌های کوچک باقی می‌ماند.» این را یهوه، خدای اسرائیل فرموده است.
7 A wannan rana mutane za su nemi Mahaliccinsu su kuma juye idanunsu ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
در آن روز، مردم به سوی آفرینندهٔ خود که خدای قدوس اسرائیل است روی خواهند آورد،
8 Ba za su dubi bagade ba, waɗanda suke aikin hannuwansu, ba za su kuma kula da ginshiƙan Ashera ba da kuma bagadan turaren da yatsotsinsu suka yi.
و دیگر به مذبحها و بتهایی که به دست خود ساخته‌اند، یعنی اشیریم و بتهای آفتاب، رو نخواهند نمود.
9 A wannan rana biranensu masu ƙarfi, waɗanda suka bari saboda Isra’ilawa, za su zama kamar wuraren da aka ƙyale suka zama kufai a jeji. Za su kuma zama kango.
در آن روز، شهرهای مستحکم ویران خواهند شد همچون شهرهای حوی‌ها و اموری‌ها که ساکنانشان آنها را در حین فرار برای اسرائیلی‌ها واگذاشتند.
10 Kun manta da Allah Mai Cetonku; ba ku tuna da Dutse, kagararku ba. Saboda haka, ko da yake kun fita ku shuka tsire-tsire mafi kyau kuka kuma shuka inabin da aka sayo daga waje,
ای اسرائیل، تو خدای نجا‌ت‌دهندۀ خود و صخرهٔ مستحکم خویش را فراموش کرده‌ای و درختان می‌کاری تا در زیر آنها بتها را بپرستی.
11 ko da yake a ranar kun shuka su, kuka sa su yi girma, da safe kuma sa’ad da kuka shuka su, kuka sa suka yi toho suka yi fure, duk da haka girbin ba zai zama kome ba a ranar cuta da zafin da ba ta da magani.
ولی بدان که حتی اگر در همان روزی که درختان را می‌کاری آنها نمو کرده، شکوفه آورند، با وجود این محصولی نخواهند داد. در آن روز، آنچه نصیب شما می‌شود بلای کشنده و درد علاج‌ناپذیر خواهد بود.
12 Kash, ga hayaniyar al’ummai masu yawa suna hayaniya kamar rurin teku! Kash, ga fushin mutane suna ruri kamar rugugi kamar manyan ruwaye!
قومهای جهان مثل دریا می‌خروشند و همچون طوفان غرش می‌کنند
13 Ko da yake mutane suna ruri kamar sukuwar raƙuman ruwa, sa’ad da ya tsawata musu za su gudu can da nisa, aka kore su kamar yayinda iska ya hura a kan tuddai, kamar tattake kuma a cikin guguwa.
و مانند سیل یورش می‌آورند. اما خدا آنها را خاموش می‌کند و به عقب می‌راند. ایشان مانند کاه در برابر باد، و خاک در برابر گردباد هستند.
14 Da yamma, sai razana ba tsammani! Kafin safiya, duk sun ɓace! Wannan ne rabon waɗanda suka washe mu, rabon waɗanda suka yi mana ƙwace.
در شب رعب و وحشت ایجاد می‌کنند، ولی پیش از فرا رسیدن صبح نابود می‌شوند. این سزای کسانی است که سرزمین ما را تاراج می‌کنند و به یغما می‌برند.

< Ishaya 17 >