< Ishaya 17 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Damaskus. “Duba, Damaskus ba za tă ƙara zama birni ba amma za tă zama tsibin juji.
La charge de Damas; voici, Damas est détruite pour n'être plus ville, et elle ne sera qu'un monceau de ruines.
2 Za a watse a bar biranen Arower a bar wa tumaki da shanu, waɗanda za su kwanta, ba tare da wani wanda zai tsorata su ba.
Les villes de Haroher seront abandonnées, elles deviendront des parcs de brebis qui y reposeront, et il n'y aura personne qui les épouvante.
3 Birni mai katanga za tă ɓace daga Efraim, ikon sarauta kuma daga Damaskus; raguwar Aram za tă zama kamar darajar Isra’ila,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Il n'y aura point de forteresse en Ephraïm, ni de Royaume à Damas, ni dans le reste de la Syrie; ils seront comme la gloire des enfants d'Israël, dit l'Eternel des armées.
4 “A wannan rana ɗaukakar Yaƙub za tă ƙare; kitsen jikinsa zai lalace.
Et il arrivera en ce jour-là, que la gloire de Jacob sera diminuée, et que la graisse de sa chair sera fondue.
5 Zai zama kamar sa’ad da mai girbi ya tara hatsin da yake tsaye ya kuma girbe hatsin da hannunsa kamar sa’ad da mutum ya yi kala kawunan hatsi a Kwarin Refayim.
Et il [en] arrivera comme quand le moissonneur cueille les blés, et qu'il moissonne les épis avec son bras; il [en] arrivera, dis-je, comme quand on ramasse les épis dans la vallée des Réphaïns.
6 Duk da haka waɗansu kala za su ragu, sai ka ce sa’ad da an karkaɗe itace zaitun, aka bar’ya’yan zaitun biyu ko uku a can ƙwanƙolin rassan, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassa na gefe na itace mai’ya’ya,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Mais il y demeurera quelques grappillages, comme quand on secoue l'olivier, et qu'il reste deux ou trois olives au bout des plus hautes branches, et qu'il y en a quatre ou cinq que l'olivier a produites dans ses branches fruitières, dit l'Eternel, le Dieu d'Israël.
7 A wannan rana mutane za su nemi Mahaliccinsu su kuma juye idanunsu ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
En ce jour-là, l'homme tournera sa vue vers celui qui l'a fait, et ses yeux regarderont vers le Saint d'Israël.
8 Ba za su dubi bagade ba, waɗanda suke aikin hannuwansu, ba za su kuma kula da ginshiƙan Ashera ba da kuma bagadan turaren da yatsotsinsu suka yi.
Et il ne jettera plus sa vue vers les autels qui sont l'ouvrage de ses mains, et ne regardera plus ce que ses doigts auront fait, ni les bocages, ni les tabernacles.
9 A wannan rana biranensu masu ƙarfi, waɗanda suka bari saboda Isra’ilawa, za su zama kamar wuraren da aka ƙyale suka zama kufai a jeji. Za su kuma zama kango.
En ce jour-là, les villes de sa force, qui auront été abandonnées à cause des enfants d'Israël, seront comme un bois taillis et des rameaux abandonnés, et il y aura désolation.
10 Kun manta da Allah Mai Cetonku; ba ku tuna da Dutse, kagararku ba. Saboda haka, ko da yake kun fita ku shuka tsire-tsire mafi kyau kuka kuma shuka inabin da aka sayo daga waje,
Parce que tu as oublié le Dieu de ton salut, et que tu ne t'es point souvenue du rocher de ta force, à cause de cela tu as transplanté des plantes [tirées des lieux] de plaisance, et tu as planté des provins d'un pays étranger.
11 ko da yake a ranar kun shuka su, kuka sa su yi girma, da safe kuma sa’ad da kuka shuka su, kuka sa suka yi toho suka yi fure, duk da haka girbin ba zai zama kome ba a ranar cuta da zafin da ba ta da magani.
De jour tu auras fait croître ce que tu auras planté, et le matin tu auras fait lever ta semence; [mais] la moisson sera enlevée au jour que l'on voulait en jouir, et il y aura une douleur désespérée.
12 Kash, ga hayaniyar al’ummai masu yawa suna hayaniya kamar rurin teku! Kash, ga fushin mutane suna ruri kamar rugugi kamar manyan ruwaye!
Malheur à la multitude de plusieurs peuples qui bruient comme bruient les mers; et à la tempête éclatante des nations, qui font du bruit comme une tempête éclatante d'eaux impétueuses.
13 Ko da yake mutane suna ruri kamar sukuwar raƙuman ruwa, sa’ad da ya tsawata musu za su gudu can da nisa, aka kore su kamar yayinda iska ya hura a kan tuddai, kamar tattake kuma a cikin guguwa.
Les nations bruient comme une tempête éclatante de grosses eaux, mais il la menacera, et elle s'enfuira loin; elle sera poursuivie comme la balle des montagnes, chassée par le vent, et comme une boule poussée par un tourbillon.
14 Da yamma, sai razana ba tsammani! Kafin safiya, duk sun ɓace! Wannan ne rabon waɗanda suka washe mu, rabon waɗanda suka yi mana ƙwace.
Au temps du soir voici l'épouvante, mais avant le matin il ne sera plus; c'est là la portion de ceux qui nous auront fourragés, et le lot de ceux qui nous auront pillés.

< Ishaya 17 >