< Ishaya 17 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Damaskus. “Duba, Damaskus ba za tă ƙara zama birni ba amma za tă zama tsibin juji.
The burden of Damascus. Behold Damascus shall cease to be a city, and shall be as a ruinous heap of stones.
2 Za a watse a bar biranen Arower a bar wa tumaki da shanu, waɗanda za su kwanta, ba tare da wani wanda zai tsorata su ba.
The cities of Aroer shall be left for flocks, and they shall rest there, and there shall be none to make them afraid.
3 Birni mai katanga za tă ɓace daga Efraim, ikon sarauta kuma daga Damaskus; raguwar Aram za tă zama kamar darajar Isra’ila,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And aid shall cease from Ephraim, and the kingdom from Damascus: and the remnant of Syria shall be as the glory of the children of Israel: saith the Lord of hosts.
4 “A wannan rana ɗaukakar Yaƙub za tă ƙare; kitsen jikinsa zai lalace.
And it shall come to pass in that day, that the glory of Jacob shall be made thin, and the fatness of his flesh shall grow lean.
5 Zai zama kamar sa’ad da mai girbi ya tara hatsin da yake tsaye ya kuma girbe hatsin da hannunsa kamar sa’ad da mutum ya yi kala kawunan hatsi a Kwarin Refayim.
And it shall be as when one gathereth in the harvest that which remaineth, and his arm shall gather the ears of corn: and it shall be as he that seeketh ears in the vale of Raphaim.
6 Duk da haka waɗansu kala za su ragu, sai ka ce sa’ad da an karkaɗe itace zaitun, aka bar’ya’yan zaitun biyu ko uku a can ƙwanƙolin rassan, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassa na gefe na itace mai’ya’ya,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And the fruit thereof that shall be left upon it, shall be as one cluster of grapes, and as the shaking of the olive tree, two or three berries in the top of a bough, or four or five upon the top of the tree, saith the Lord the God of Israel.
7 A wannan rana mutane za su nemi Mahaliccinsu su kuma juye idanunsu ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
In that day man shall bow down himself to his Maker, and his eyes shall look to the Holy One of Israel.
8 Ba za su dubi bagade ba, waɗanda suke aikin hannuwansu, ba za su kuma kula da ginshiƙan Ashera ba da kuma bagadan turaren da yatsotsinsu suka yi.
And he shall not look to the altars which his hands made: and he shall not have respect to the things that his fingers wrought, such as groves and temples.
9 A wannan rana biranensu masu ƙarfi, waɗanda suka bari saboda Isra’ilawa, za su zama kamar wuraren da aka ƙyale suka zama kufai a jeji. Za su kuma zama kango.
In that day his strong cities shall be forsaken, as the ploughs, and the corn that were left before the face of the children of Israel, and thou shalt be desolate.
10 Kun manta da Allah Mai Cetonku; ba ku tuna da Dutse, kagararku ba. Saboda haka, ko da yake kun fita ku shuka tsire-tsire mafi kyau kuka kuma shuka inabin da aka sayo daga waje,
Because thou hast forgotten God thy saviour, and hast not remembered thy strong helper: therefore shalt thou plant good plants, and shalt sow strange seed.
11 ko da yake a ranar kun shuka su, kuka sa su yi girma, da safe kuma sa’ad da kuka shuka su, kuka sa suka yi toho suka yi fure, duk da haka girbin ba zai zama kome ba a ranar cuta da zafin da ba ta da magani.
In the day of thy planting shall be the wild grape, and in the morning thy seed shall flourish: the harvest is taken away in the day of inheritance, and shall grieve thee much.
12 Kash, ga hayaniyar al’ummai masu yawa suna hayaniya kamar rurin teku! Kash, ga fushin mutane suna ruri kamar rugugi kamar manyan ruwaye!
Woe to the multitude of many people, like the multitude of the roaring sea: and the tumult of crowds, like the noise of many waters.
13 Ko da yake mutane suna ruri kamar sukuwar raƙuman ruwa, sa’ad da ya tsawata musu za su gudu can da nisa, aka kore su kamar yayinda iska ya hura a kan tuddai, kamar tattake kuma a cikin guguwa.
Nations shall make a noise like the noise of waters overflowing, but he shall rebuke him, and he shall flee far off: and he shall be carried away as the dust of the mountains before the wind, and as a whirlwind before a tempest.
14 Da yamma, sai razana ba tsammani! Kafin safiya, duk sun ɓace! Wannan ne rabon waɗanda suka washe mu, rabon waɗanda suka yi mana ƙwace.
In the time of the evening, behold there shall be trouble: the morning shall come, and he shall not be: this is the portion of them that have wasted us, and the lot of them that spoiled us.

< Ishaya 17 >