< Ishaya 17 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Damaskus. “Duba, Damaskus ba za tă ƙara zama birni ba amma za tă zama tsibin juji.
Profeti imod Damaskus. Se, Damaskus skal ikke mere være en Stad, men den skal være en sammenstyrtet Stenhob.
2 Za a watse a bar biranen Arower a bar wa tumaki da shanu, waɗanda za su kwanta, ba tare da wani wanda zai tsorata su ba.
Aroers Stæder skulle blive forladte; de skulle være for Hjorde, og disse skulle ligge der, og ingen skal forfærde dem.
3 Birni mai katanga za tă ɓace daga Efraim, ikon sarauta kuma daga Damaskus; raguwar Aram za tă zama kamar darajar Isra’ila,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Og det skal være forbi med Befæstningen for Efraim og med Kongedømmet for Damaskus og for det overblevne af Syrerne; de skulle være som Israels Børns Herlighed, siger den Herre Zebaoth.
4 “A wannan rana ɗaukakar Yaƙub za tă ƙare; kitsen jikinsa zai lalace.
Og det skal ske paa den Dag, da skal Jakobs Herlighed blive ringe, og hans Køds Fedme skal blive mager.
5 Zai zama kamar sa’ad da mai girbi ya tara hatsin da yake tsaye ya kuma girbe hatsin da hannunsa kamar sa’ad da mutum ya yi kala kawunan hatsi a Kwarin Refayim.
Og det skal gaa, som naar en Høstmand griber om det stagende Korn, og hans Arm høster Aksene; og det skal gaa, som naar een samler Aks i Refaims Dal.
6 Duk da haka waɗansu kala za su ragu, sai ka ce sa’ad da an karkaɗe itace zaitun, aka bar’ya’yan zaitun biyu ko uku a can ƙwanƙolin rassan, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassa na gefe na itace mai’ya’ya,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Og der skal blive en Efterslet tilovers derudi, som naar man ryster et Olietræ: To eller tre Bær i den øverste Top, fire eller fem paa de frugtbare Kviste, siger Herren, Israels Gud.
7 A wannan rana mutane za su nemi Mahaliccinsu su kuma juye idanunsu ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Paa den Dag skal Mennesket se hen til den, som har skabt ham, og hans Øjne skulle se hen til den Hellige i Israel.
8 Ba za su dubi bagade ba, waɗanda suke aikin hannuwansu, ba za su kuma kula da ginshiƙan Ashera ba da kuma bagadan turaren da yatsotsinsu suka yi.
Og han skal ikke se hen til Altrene, hans Hænders Gerning, og ikke se til det, som hans Fingre have gjort, hverken til Astartes eller Solens Billeder.
9 A wannan rana biranensu masu ƙarfi, waɗanda suka bari saboda Isra’ilawa, za su zama kamar wuraren da aka ƙyale suka zama kufai a jeji. Za su kuma zama kango.
Paa den Dag skulle hans faste Stæder vorde som de forladte Skove og Højder, som man havde forladt for Israels Børns Skyld, og der skal blive en Ørk.
10 Kun manta da Allah Mai Cetonku; ba ku tuna da Dutse, kagararku ba. Saboda haka, ko da yake kun fita ku shuka tsire-tsire mafi kyau kuka kuma shuka inabin da aka sayo daga waje,
Thi du har glemt din Frelses Gud og ikke ihukommet din Styrkes Klippe; derfor planter du liflige Plantninger og besætter din Vingaard med fremmede Ranker.
11 ko da yake a ranar kun shuka su, kuka sa su yi girma, da safe kuma sa’ad da kuka shuka su, kuka sa suka yi toho suka yi fure, duk da haka girbin ba zai zama kome ba a ranar cuta da zafin da ba ta da magani.
Paa den Dag, du planter, gærder du derom, og om Morgenen bringer du din Sæd til at grønnes; men flygtet er Høsten paa Sygdommens og den ulægelige Smertes Dag.
12 Kash, ga hayaniyar al’ummai masu yawa suna hayaniya kamar rurin teku! Kash, ga fushin mutane suna ruri kamar rugugi kamar manyan ruwaye!
Ve, en Brusen af mange Folkeslag! de bruse som Havets Brusen; og et Bulder af Folkefærd! de buldre, som mægtige Vande buldre.
13 Ko da yake mutane suna ruri kamar sukuwar raƙuman ruwa, sa’ad da ya tsawata musu za su gudu can da nisa, aka kore su kamar yayinda iska ya hura a kan tuddai, kamar tattake kuma a cikin guguwa.
Folkene buldre som store Vandes Bulder, men han truer dem, saa de fly langt bort; og de bortjages som Avner paa Bjergene for Vejret og som en Hvirvel for Hvirvelvind.
14 Da yamma, sai razana ba tsammani! Kafin safiya, duk sun ɓace! Wannan ne rabon waɗanda suka washe mu, rabon waɗanda suka yi mana ƙwace.
Ved Aftenstid — se, da er der Forskrækkelse! førend Morgenen kommer, da ere de ikke mere; dette er deres Del, som plyndre os, og deres Lod, som berøve os.