< Ishaya 16 >

1 Ku aiko da raguna a matsayin haraji ga mai mulkin ƙasar, daga Sela a hamada, zuwa dutsen Diyar Sihiyona.
Y enviarán él cordero del tributo desde Sela en el desierto hasta el monte de la hija de Sión.
2 Kamar tsuntsaye masu firiya da aka kora daga sheƙa, haka matan Mowab suke a kogunan Arnon.
Porque las hijas de Moab serán como pájaros espantados, que huyen de su nido, en los caminos a través del Arnón.
3 “Ku ba mu shawara, ku yanke shawara. Ku mai da inuwarku kamar dare, a tsakar rana. Ku ɓoye masu gudun hijira, kada ku bashe masu neman mafaka.
Da instrucciones sabias, toma una decisión; que tu sombra sea como la noche en él mediodía; mantén a salvo a los que están en vuelo; No renuncies a los errantes.
4 Ku bar Mowabawa masu gudun hijira su zauna tare da ku; ku zama mafakarsu daga mai neman hallaka su.” Mai danniya zai zo ga ƙarshe hallaka kuma za tă daina; masu lalatar da ƙasa za su kare
Deja que los que han sido expulsados de Moab tengan un lugar de descanso contigo; sé una cobertura para quien está siendo desterrado; hasta que los crueles sean eliminados, y el desperdicio haya llegado a su fin, y aquellos que se complacen en aplastar a los pobres se han ido de la tierra.
5 Da ƙauna za a kafa kursiyi; da aminci mutum zai zauna a kansa, wani daga gidan Dawuda, wani wanda ta shari’antawa yakan nuna gaskiya ya hanzarta yin adalci.
Entonces el trono de un rey se basará en la misericordia, y uno se sentará en él en tabernáculo de David para siempre; juzgando rectamente, y rápido para hacer justicia.
6 Mun ji fariyar Mowab, mun ji yawan fariyarta da girmankanta, fariyarta da reninta, amma taƙamarsu ta banza ce.
Hemos tenido noticia del orgullo de Moab, cuán grande es; cómo se alza con orgullo y pasión: sus palabras elevadas sobre sí mismo son falsas.
7 Saboda haka Mowabawa za su yi kuka mai zafi, za su yi kuka mai zafi tare saboda Mowab. Ku yi makoki ku kuma yi baƙin ciki saboda ƙosai da kuka riƙa ci a Kir Hareset.
Por esta causa, todos en Moab darán gritos de dolor por Moab: por los fundamentos, llorarán por los hombres de Kir-hareset.
8 Gonakin Heshbon sun bushe, inabin Sibma ma haka. Masu mulkin al’ummai sun tattake inabi mafi kyau, waɗanda suka taɓa yaɗuwa zuwa Yazer suka bazu ta wajen hamada. Tohonsu sun buɗu suka kai har teku.
Porque los campos de Hesbón son desechos, la vid de Sibma está muerta; los señores de las naciones fueron vencidos por el producto de sus vides; sus plantas de vid llegaron hasta Jazer y llegaron hasta él desierto; sus ramas se extendían hasta el mar.
9 Saboda haka na yi kuka, yadda Yazer take kuka, saboda inabin Sibma. Ya Heshbon, ya Eleyale, na cika ku da hawaye! Sowa ta murna a kanku saboda’ya’yan itatuwanku da suka nuna da kuma girbinku sun ɓace.
Por esta causa, mi dolor por la viña de Sibma será como el llanto por Jazer: ¡derramó lágrimas sobre ti, oh Hesbón y Eleale! Porque están haciendo sonar el grito de guerra sobre tus frutos de verano y la entrada de tu grano;
10 An ɗauke farin ciki da murna daga gonakin itatuwa masu’ya’ya; babu wanda yake rerawa ko yake sowa a cikin gonakin inabi; babu wanda yake matsin ruwan inabi a wuraren matsi, gama na kawo ƙarshen yin sowa.
Y todo el gozo se ha ido; ya no se alegran por el campo fértil; y en los viñedos no hay canciones ni sonidos de alegría. Él aplastamiento de las uvas ha llegado a su fin, y su grito de alegría se ha detenido.
11 Zuciyata tana makoki saboda Mowab kamar garaya, na yi baƙin ciki saboda Kir Hareset.
Por esta causa, las cuerdas de mi corazón están sonando para Moab, y estoy lleno de pena por los Kir-hareset.
12 Sa’ad Mowab ta bayyana a masujadar bisa tudu, tana gajiyar da kanta ne kawai; sa’ad da ta tafi wurin tsafinta don tă yi addu’a, babu wani amfani.
Y cuando Moab suba al lugar alto y haga oración en la casa de su dios, no tendrá efecto.
13 Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya riga ya yi game da Mowab.
Esta es la palabra que el Señor dijo acerca de Moab en el pasado.
14 Amma yanzu Ubangiji ya ce, “Cikin shekara uku, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, haka za a mai da daraja da kuma dukan yawan mutanen Mowab abin reni, daga ɗumbun mutanenta,’yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”
Pero ahora el Señor ha dicho: En tres años, los años de un siervo que trabaja para el pago, la gloria de Moab, toda esa gran gente, se convertirá en vergüenza, y el resto de Moab será muy pequeño y sin honor.

< Ishaya 16 >