< Ishaya 16 >

1 Ku aiko da raguna a matsayin haraji ga mai mulkin ƙasar, daga Sela a hamada, zuwa dutsen Diyar Sihiyona.
Envoyez les agneaux pour le chef du pays, de Sélah au désert, à la montagne de la fille de Sion.
2 Kamar tsuntsaye masu firiya da aka kora daga sheƙa, haka matan Mowab suke a kogunan Arnon.
Car, comme des oiseaux errants, comme un nid dispersé, ainsi seront les filles de Moab aux gués de l'Arnon.
3 “Ku ba mu shawara, ku yanke shawara. Ku mai da inuwarku kamar dare, a tsakar rana. Ku ɓoye masu gudun hijira, kada ku bashe masu neman mafaka.
Donnez des conseils! Rendez la justice! Fais ton ombre comme la nuit au milieu du midi! Cache les proscrits! Ne trahis pas le fugitif!
4 Ku bar Mowabawa masu gudun hijira su zauna tare da ku; ku zama mafakarsu daga mai neman hallaka su.” Mai danniya zai zo ga ƙarshe hallaka kuma za tă daina; masu lalatar da ƙasa za su kare
Laisse mes exilés habiter chez toi! Quant à Moab, sois pour lui un refuge contre la face du destructeur. Car l'extorqueur est réduit à néant. La destruction cesse. Les oppresseurs sont consumés hors du pays.
5 Da ƙauna za a kafa kursiyi; da aminci mutum zai zauna a kansa, wani daga gidan Dawuda, wani wanda ta shari’antawa yakan nuna gaskiya ya hanzarta yin adalci.
Un trône sera établi dans la bonté. Un homme s'y assiéra dans la vérité, dans la tente de David, jugeant, recherchant la justice, et prompt à pratiquer la droiture.
6 Mun ji fariyar Mowab, mun ji yawan fariyarta da girmankanta, fariyarta da reninta, amma taƙamarsu ta banza ce.
Nous avons entendu parler de l'orgueil de Moab, de sa grande fierté, de son arrogance, de son orgueil et de sa colère. Ses fanfaronnades ne sont rien.
7 Saboda haka Mowabawa za su yi kuka mai zafi, za su yi kuka mai zafi tare saboda Mowab. Ku yi makoki ku kuma yi baƙin ciki saboda ƙosai da kuka riƙa ci a Kir Hareset.
C'est pourquoi Moab se lamentera sur Moab. Tout le monde se lamentera. Vous pleurerez sur les gâteaux de Kir Hareseth, frappés de mort.
8 Gonakin Heshbon sun bushe, inabin Sibma ma haka. Masu mulkin al’ummai sun tattake inabi mafi kyau, waɗanda suka taɓa yaɗuwa zuwa Yazer suka bazu ta wajen hamada. Tohonsu sun buɗu suka kai har teku.
Car les champs de Hesbon languissent avec la vigne de Sibma. Les seigneurs des nations ont brisé ses sarments de choix, qui atteignaient jusqu'à Jazer, qui s'égaraient dans le désert. Ses sarments se sont répandus. Elles passaient au-dessus de la mer.
9 Saboda haka na yi kuka, yadda Yazer take kuka, saboda inabin Sibma. Ya Heshbon, ya Eleyale, na cika ku da hawaye! Sowa ta murna a kanku saboda’ya’yan itatuwanku da suka nuna da kuma girbinku sun ɓace.
C'est pourquoi je pleurerai avec les pleurs de Jaezer sur la vigne de Sibma. Je t'arroserai de mes larmes, Hesbon et Élealé; car sur tes fruits d'été et sur ta moisson est tombé le cri de guerre.
10 An ɗauke farin ciki da murna daga gonakin itatuwa masu’ya’ya; babu wanda yake rerawa ko yake sowa a cikin gonakin inabi; babu wanda yake matsin ruwan inabi a wuraren matsi, gama na kawo ƙarshen yin sowa.
L'allégresse a disparu, la joie s'est retirée du champ fructueux; dans les vignes, il n'y aura plus de chant, plus de bruit joyeux. Personne ne foulera le vin dans les pressoirs. J'ai fait cesser les cris.
11 Zuciyata tana makoki saboda Mowab kamar garaya, na yi baƙin ciki saboda Kir Hareset.
C'est pourquoi mon cœur résonne comme une harpe pour Moab, et mes entrailles pour Kir Hérès.
12 Sa’ad Mowab ta bayyana a masujadar bisa tudu, tana gajiyar da kanta ne kawai; sa’ad da ta tafi wurin tsafinta don tă yi addu’a, babu wani amfani.
Quand Moab se présentera, quand il se fatiguera sur le haut lieu, quand il viendra prier dans son sanctuaire, il ne prévaudra pas.
13 Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya riga ya yi game da Mowab.
Telle est la parole que l'Éternel a prononcée autrefois sur Moab.
14 Amma yanzu Ubangiji ya ce, “Cikin shekara uku, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, haka za a mai da daraja da kuma dukan yawan mutanen Mowab abin reni, daga ɗumbun mutanenta,’yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”
Mais maintenant, l'Éternel a parlé, en disant: « Dans trois ans, comme un ouvrier lié par contrat les compterait, la gloire de Moab sera méprisée, avec toute sa grande multitude; et le reste sera très petit et faible. »

< Ishaya 16 >