< Ishaya 15 >
1 Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
Malheur accablant de Moab. Parce que pendant la nuit Ar a été dévastée, Moab s’est tu; parce que pendant la nuit a été détruit le mur, Moab s’est tu.
2 Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
La maison et Dibon sont montées sur les hauts lieux pour pleurer sur Nabo et sur Médaba; Moab a poussé des hurlements; sur toutes les têtes sera la calvitie, et toute barbe sera rasée.
3 A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
Dans ses rues ils ont été vêtus de sacs; sur ses toits tout hurlement est descendu dans le pleur.
4 Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
Hésébon et Eléalé crieront; jusqu’à Jasa leur voix a été entendue; à cause de cela les vaillant de Moab hurleront; et son âme hurlera pour elle-même.
5 Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
Mon cœur pour Moab criera; ses verrous se feront entendre jusqu’à Ségor, génisse de trois ans; car par la montée de Luith ils monteront en pleurant, et dans la voix d’Oronaïm ils élèveront le cri d’une douleur déchirante.
6 Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
Car les eaux de Nemrim deviendront un désert, parce que l’herbe s’est desséchée, que le bourgeon a manqué et que toute verdure a péri.
7 Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
Selon la grandeur de leurs œuvres, tel sera leur châtiment; au torrent des saules on les conduira.
8 Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
Parce que le cri parcourra la frontière de Moab; jusqu’à Gallim ira son hurlement, jusqu’au Puits d’Elim son cri.
9 Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.
Parce que les eaux de Dibon ont été remplies de sang; car j’enverrai sur Dibon un surcroît de châtiment; à ceux qui fuiront de Moab et aux restes de cette terre, un lion.