< Ishaya 15 >

1 Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
La charge de Moab; parce que Har de Moab a été ravagée de nuit, il a été défait; parce que Kir de Moab a été saccagée de nuit, il a été défait.
2 Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
Il est monté à Bajith, et à Dibon, dans les hauts lieux, pour pleurer; Moab hurlera sur Nébo, et sur Médeba, toutes ses têtes seront chauves, et toute barbe sera rasée.
3 A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
On sera ceint de sacs dans ses rues, chacun hurlera fondant en larmes sur ses toits, et dans ses places.
4 Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
Hesbon et Elhalé se sont écriées, leur voix a été ouïe jusqu'à Jahats; c'est pourquoi ceux de Moab qui seront équipés [pour aller à la guerre], jetteront des cris lamentables, son âme se tourmentera au dedans de lui.
5 Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
Mon cœur crie à cause de Moab; ses fugitifs s'en sont fuis jusqu'à Tsohar, [comme] une génisse de trois ans; car on montera par la montée de Luhith avec des pleurs, et on fera retentir le cri de la plaie au chemin de Horonajim.
6 Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
Même les eaux de Nimrim ne seront que désolations, même le foin est déjà séché, l'herbe a été consumée, et il n'y a point de verdure.
7 Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
Il aura acquis des richesses en abondance, afin que ce qu'ils auront réservé soit porté dans la vallée des Arabes.
8 Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
Car le cri a environné la contrée de Moab; son hurlement [ira] jusqu'à Eglajim, et son hurlement jusqu'à Béer-Elim.
9 Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.
Même les eaux de Dimon ont été remplies de sang; car j'ajouterai un surcroît sur Dimon, [savoir] le lion à ceux qui seront réchappés de Moab, et au résidu du pays.

< Ishaya 15 >