< Ishaya 15 >
1 Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
Le fardeau de Moab. Car en une nuit, Ar de Moab est dévasté et réduit à néant. Car en une nuit, Ar de Moab est dévasté et réduit à néant.
2 Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
Ils sont montés à Bayith et à Dibon, sur les hauts lieux, pour pleurer. Moab gémit sur Nebo et sur Medeba. La calvitie est sur toutes leurs têtes. Toute barbe est coupée.
3 A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
Dans leurs rues, ils se revêtent de sacs. Dans leurs rues et sur leurs toits, tous gémissent et pleurent abondamment.
4 Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
Hesbon crie avec Élealé. Leur voix se fait entendre jusqu'à Jahaz. C'est pourquoi les hommes armés de Moab crient à haute voix. Leurs âmes tremblent au dedans d'eux.
5 Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
Mon cœur pleure sur Moab! Ses nobles fuient vers Tsoar, vers Églath-Shelishiyah; car ils montent en pleurant par la montée de Luhith; car sur le chemin des Horonaïm, ils poussent des cris de destruction.
6 Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
Car les eaux de Nimrim seront désolées; car l'herbe s'est desséchée, l'herbe tendre se fane, il n'y a plus rien de vert.
7 Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
C'est pourquoi ils emporteront l'abondance qu'ils ont acquise, et ce qu'ils ont amassé, sur le ruisseau des saules.
8 Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
Car le cri a fait le tour des frontières de Moab, son gémissement jusqu'à Églaïm, et sa plainte jusqu'à Beer Elim.
9 Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.
Car les eaux de Dimon sont pleines de sang; car je fais venir encore sur Dimon, un lion sur ceux de Moab qui s'échappent, et sur le reste du pays.