< Ishaya 15 >
1 Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
The doom of Moab. Truly in a night is 'Ar of Moab plundered, it is laid waste; truly in a night is Kir of Moab plundered, it is laid waste.
2 Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
It goeth up to the [idol-]house, and Dibon [goeth] up to the high-places to weep, on Nebo and on Medeba shall Moab wail: on all its heads there is baldness, and every beard is hewn off.
3 A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
In its streets they are girded with sack-cloth, on its roofs, and in its public places every one shall wail, groan with weeping.
4 Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
And loud crieth Cheshbon with El'aleh; as far as Yahaz is heard their voice: therefore the armed men of Moab shall howl; its soul is grieved for itself.
5 Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
My heart will cry for Moab, whose fugitives are as far as Zo'ar, [and] the third 'Eglarth; for the ascent of Luchith—with weeping is it ascended; for on the way to Choronayim they let resound the cry of defeat [in battle].
6 Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
For the waters of Nimrim shall be desolate; for dry is the grass, gone are the herbs, and green things are no more.
7 Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
Therefore the rest of their acquisitions and what they possess shall they carry away over the brook of the willows.
8 Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
For the cry hath encompassed the boundary of Moab; up to Eglayim [is heard] its wail, and at Beer-elim [is heard] its wail.
9 Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.
For the waters of Dimon are filled with blood; for I will bring over Dimon armed bands; over the escaped of Moab [cometh] a lion, and over the remnant of the land.