< Ishaya 15 >

1 Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
The burden of Moab. Because in the night Ar of Moab is laid waste, it is silent: because the wall of Moab is destroyed in the night, it is silent.
2 Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
The house is gone up, and Dibon to the high places to mourn over Nabo, and over Medaba, Moab hath howled: ton all their heads shall be baldness, and every beard shall be shaven.
3 A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
In their streets they are girded with sackcloth: on the tops of their houses, and in their streets all shall howl and come down weeping.
4 Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
Hesebon shall cry, and Eleale, their voice is heard even to Jasa. For this shall the well appointed men of Moab howl, his soul shall howl to itself.
5 Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
My heart shall cry to Moab, the bars thereof shall flee unto Segor a heifer of three years old: for by the ascent of Luith they shall go up weeping: and in the way of Oronaim they shall lift up a cry of destruction.
6 Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
For the waters of Nemrim shall be desolate, for the grass is withered away, the spring is faded, all the greenness is perished.
7 Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
According to the greatness of their work, is their visitation also: they shall lead them to the torrent of the willows.
8 Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
For the cry is gone round about the border of Moab: the howling thereof unto Gallim, and unto the well of Elim the cry thereof.
9 Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.
For the waters of Dibon are filled with blood: for I will bring more upon Dibon: the lion upon them that shall flee of Moab, and upon the remnant of the land.

< Ishaya 15 >