< Ishaya 14 >

1 Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
Porque el Señor se compadecerá de Jacob, y aún escogerá a Israel, y lo pondrá en su propia tierra. El extranjero se unirá a ellos, y ellos se unirán a la casa de Jacob.
2 Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
Los pueblos los tomarán y los llevarán a su lugar. La casa de Israel los poseerá en la tierra de Yahvé como siervos y siervas. Tomarán como cautivos a los que fueron cautivos; y gobernarán a sus opresores.
3 A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
Sucederá en el día en que Yahvé te dé descanso de tu dolor, de tu angustia y del duro servicio en el que te hicieron servir,
4 za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
que tomarás esta parábola contra el rey de Babilonia, y dirás: “¡Cómo ha cesado el opresor! La ciudad de oro ha cesado!”
5 Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
Yahvé ha quebrado el báculo de los malvados, el cetro de los gobernantes,
6 wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
que golpeaban con ira a los pueblos con un golpe continuo, que gobernaban a las naciones con ira, con una persecución que nadie frenaba.
7 Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
Toda la tierra descansa y se aquieta. Prorrumpen en cánticos.
8 Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
Sí, los cipreses se alegran contigo, con los cedros del Líbano, diciendo: “Desde que te humillaste, ningún leñador ha subido contra nosotros.”
9 Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
El Seol de abajo se ha movido por ti para recibirte en tu llegada. Se agita los espíritus difuntos para usted, incluso todos los gobernantes de la tierra. Ha levantado de sus tronos a todos los reyes de las naciones. (Sheol h7585)
10 Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
Todos ellos responderán y te preguntarán: “¿Te has vuelto tan débil como nosotros? ¿Os habéis vuelto como nosotros?”
11 An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
Tu pompa desciende al Seol, con el sonido de tus instrumentos de cuerda. Los gusanos se extienden debajo de ti, y los gusanos te cubren. (Sheol h7585)
12 Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
¡Cómo has caído del cielo, resplandeciente, hijo de la aurora! ¡Cómo has sido derribado al suelo, el que abatió a las naciones!
13 Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
Dijiste en tu corazón: “¡Subiré al cielo! ¡Exaltaré mi trono por encima de las estrellas de Dios! Me sentaré en el monte de la asamblea, en el lejano norte.
14 Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
¡Subiré a las alturas de las nubes! Me haré semejante al Altísimo”.
15 Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
Sin embargo, serás llevado al Seol, a las profundidades de la fosa. (Sheol h7585)
16 Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
Los que te vean te mirarán fijamente. Te meditarán, diciendo: “¿Es éste el hombre que hizo temblar la tierra, que hizo temblar los reinos,
17 mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
que convirtió el mundo en un desierto y asoló sus ciudades, que no liberó a sus prisioneros a su hogar?”
18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
Todos los reyes de las naciones duermen en la gloria, cada uno en su casa.
19 Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
Pero tú eres arrojado de tu tumba como una rama abominable, vestido con los muertos que son atravesados por la espada, que descienden a las piedras de la fosa; como un cadáver pisoteado.
20 ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
No te unirás a ellos en la sepultura, porque has destruido tu tierra. Has matado a tu pueblo. La descendencia de los malhechores no será nombrada para siempre.
21 A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
Prepara la matanza de sus hijos a causa de la iniquidad de sus padres, para que no se levanten y posean la tierra y llenen de ciudades la superficie del mundo.
22 “Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
“Me levantaré contra ellos — dice el Señor de los Ejércitos — y cortaré de Babilonia el nombre y el remanente, el hijo y el hijo del hijo — dice el Señor —
23 “Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
“También la convertiré en una posesión para el puercoespín, y en estanques de agua. La barreré con la escoba de la destrucción”, dice el Señor de los Ejércitos.
24 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
El Señor de los Ejércitos ha jurado, diciendo: “Ciertamente, como lo he pensado, así sucederá; y como lo he propuesto, así será:
25 Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
que quebraré al asirio en mi tierra, y lo pisotearé en mis montes. Entonces su yugo los abandonará, y su carga dejará sus hombros.
26 Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
Este es el plan que está determinado para toda la tierra. Esta es la mano que está extendida sobre todas las naciones.
27 Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
Porque el Señor de los Ejércitos ha planeado, y ¿quién puede detenerlo? Su mano está extendida, ¿y quién podrá hacerla retroceder?”
28 Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
Esta carga fue en el año en que murió el rey Acaz.
29 Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
No os alegréis, oh Filistea, todos vosotros, porque la vara que os golpeaba se ha quebrado; porque de la raíz de la serpiente saldrá una víbora, y su fruto será una serpiente ardiente y voladora.
30 Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
Los primogénitos de los pobres comerán, y los necesitados se acostarán con seguridad; y yo mataré tu raíz con el hambre, y tu remanente morirá.
31 Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
¡Aúlla, puerta! ¡Grita, ciudad! Os habéis derretido, Filistea, todos vosotros; porque el humo sale del norte, y no hay ningún rezagado en sus filas.
32 Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”
¿Qué responderán a los mensajeros de la nación? Que Yahvé ha fundado Sión, y en ella se refugiarán los afligidos de su pueblo.

< Ishaya 14 >