< Ishaya 14 >

1 Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
Car l’Éternel aura compassion de Jacob et choisira encore Israël, et les établira en repos sur leur terre; et l’étranger se joindra à eux, et sera ajouté à la maison de Jacob.
2 Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
Et les peuples les prendront et les feront venir en leur lieu, et la maison d’Israël les possédera, sur la terre de l’Éternel, pour serviteurs et pour servantes: et ils mèneront captifs ceux qui les tenaient captifs, et ils domineront sur leurs oppresseurs.
3 A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
Et il arrivera, au jour où l’Éternel te donnera du repos de ton labeur et de ton trouble et du dur service auquel on t’a asservi,
4 za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
que tu prononceras ce cantique sentencieux sur le roi de Babylone, et tu diras: Comment l’oppresseur a-t-il cessé? comment l’exactrice a-t-elle cessé?
5 Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
L’Éternel a brisé le bâton des méchants, le sceptre des dominateurs.
6 wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
Celui qui, dans sa fureur, frappait de coups les peuples, sans relâche, dominant les nations dans sa colère, est poursuivi sans trêve.
7 Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
Toute la terre est en repos [et] tranquille; elle éclate en chants de triomphe.
8 Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
Les cyprès aussi se réjouissent de toi, les cèdres du Liban: Depuis que tu es tombé, l’abatteur n’est plus monté contre nous!
9 Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
– Le shéol d’en bas s’émeut pour toi, te rencontrant à ta venue, réveillant pour toi les trépassés, tous les boucs de la terre, faisant lever de leurs trônes tous les rois des nations. (Sheol h7585)
10 Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
Tous, ils prendront la parole et te diront: Toi aussi, tu as été rendu faible, comme nous; tu es devenu semblable à nous.
11 An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
– Ton orgueil est descendu dans le shéol, le son de tes luths. Les vers sont étendus sous toi, et les larves sont ta couverture. (Sheol h7585)
12 Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
Comment es-tu tombé des cieux, astre brillant, fils de l’aurore? Tu es abattu jusqu’à terre, toi qui subjuguais les nations!
13 Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
Et toi, tu as dit dans ton cœur: Je monterai aux cieux, j’élèverai mon trône au-dessus des étoiles de Dieu, et je m’assiérai sur la montagne de l’assignation, au fond du nord.
14 Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
Je monterai sur les hauteurs des nues, je serai semblable au Très-haut.
15 Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
Toutefois, on t’a fait descendre dans le shéol, au fond de la fosse. (Sheol h7585)
16 Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
Ceux qui te voient fixent leurs regards sur toi, ils te considèrent, [disant]: Est-ce ici l’homme qui a fait trembler la terre, qui ébranlait les royaumes,
17 mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
qui a fait du monde un désert, et qui ruinait ses villes? Ses prisonniers, il ne les renvoyait pas chez eux.
18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
– Tous les rois des nations, eux tous, reposent dans leur gloire, chacun dans sa maison;
19 Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
mais toi, tu as été jeté hors de ton sépulcre comme une branche qui fait horreur, recouvert de tués, percés par l’épée, descendus jusqu’aux pierres d’une fosse, … comme un cadavre foulé aux pieds.
20 ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
Tu ne seras pas réuni avec eux dans le sépulcre; car tu as ruiné ton pays, tu as tué ton peuple. De la race des méchants il ne sera jamais fait mention.
21 A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
Préparez la tuerie pour ses fils, à cause de l’iniquité de leurs pères; qu’ils ne se lèvent pas, ni ne possèdent la terre, ni ne remplissent de villes la face du monde!
22 “Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
Je me lèverai contre eux, dit l’Éternel des armées, et je retrancherai de Babylone le nom et le reste, enfants et postérité, dit l’Éternel;
23 “Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
et j’en ferai une possession du butor, et des mares d’eau; et je la balaierai avec le balai de la destruction, dit l’Éternel des armées.
24 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
L’Éternel des armées a juré, disant: Pour certain, comme j’ai pensé, ainsi il arrivera, et, comme j’ai pris conseil, la chose s’accomplira,
25 Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
de briser l’Assyrien dans mon pays; et je le foulerai aux pieds sur mes montagnes; et son joug sera ôté de dessus eux, et son fardeau sera ôté de dessus leurs épaules.
26 Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
C’est là le conseil qui est arrêté contre toute la terre, et c’est là la main qui est étendue sur toutes les nations.
27 Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
Car l’Éternel des armées a pris [ce] conseil, et qui l’annulera? Et sa main est étendue, et qui la [lui] fera retirer?
28 Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
L’année de la mort du roi Achaz, fut [prononcé] cet oracle:
29 Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
Ne te réjouis pas, Philistie tout entière, de ce que la verge qui t’a frappée est brisée; car de la racine du serpent sortira une vipère, et son fruit sera un serpent brûlant qui vole;
30 Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
et les premiers-nés des misérables paîtront, et les pauvres se coucheront en assurance; mais je ferai mourir de faim ta racine, et tes restes, on les tuera.
31 Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
Hurle, porte! Ville, pousse des cris! Sois dissoute, Philistie tout entière! car une fumée vient du nord, et nul ne reste à l’écart dans ses rassemblements de troupes.
32 Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”
Et que répondra-t-on aux messagers des nations? Que l’Éternel a fondé Sion, et que les pauvres de son peuple y trouvent un refuge.

< Ishaya 14 >