< Ishaya 14 >

1 Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
For Jehovah will have compassion upon Jacob, And will again set his love upon Israel, And cause them to rest in his own land. And strangers shall join themselves to them, And cleave to the house of Jacob.
2 Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
The nations shall take them and bring them to their own place; And the house of Israel shall possess them, in the land of Jehovah, As servants and as handmaids; They shall take captive their captors, And they shall rule over their oppressors.
3 A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
So when Jehovah shall have given thee rest From thy sorrow and thy distress, And from the hard bondage Which was laid upon thee,
4 za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
Then shall thou utter this song over the king of Babylon, and say, “How hath the tyrant fallen, The oppression ceased!
5 Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
Jehovah hath broken the staff of the wicked, The rod of the tyrants,
6 wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
That smote the people in anger, With a continual stroke, That lorded it over the nations in wrath With unremitted oppression.
7 Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
The whole earth is at rest, is quiet; They break forth into singing.
8 Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
Even the cypress-trees exult over thee, And the cedars of Lebanon: 'Since thou art fallen, No feller cometh up against us.'
9 Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
The under-world is in commotion on account of thee, To meet thee at thy coming; It stirreth up before thee the shades, all the mighty of the earth; It arouseth from their thrones all the kings of the nations; (Sheol h7585)
10 Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
They all accost thee, and say, 'Art thou, too, become weak as we? Art thou become like us?'
11 An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
Thy pomp is brought down to the grave, And the sound of thy harps. Vermin have become thy couch, And worms thy covering. (Sheol h7585)
12 Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
How art thou fallen from heaven, O Lucifer, son of the morning! How art thou cast down to the ground, Thou that didst trample upon the nations!
13 Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
Thou saidst in thy heart, 'I will ascend to heaven, Above the stars of God will I exalt my throne; I will sit upon the mount of assembly in the recesses of the north.
14 Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
I will ascend above the height of the clouds; I will be like the Most High.'
15 Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
But thou art brought down to the grave, To the depths of the pit. (Sheol h7585)
16 Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
They that see thee gaze upon thee, and view thee attentively, (and say, ) 'Is this the man that made the earth tremble, That shook kingdoms,
17 mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
That made the world a wilderness, And laid waste its cities, And sent not his captives to their homes?'
18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
All the kings of the nations, yea, all of them, Lie down in glory, each in his own sepulchre;
19 Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
But thou art cast forth without a grave, Like a worthless branch; Covered with the slain, who are pierced by the sword, Who go down to the stones of the pit, Like a carcass trampled under foot.
20 ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
Thou shalt not be joined with them in the grave, Because thou hast destroyed thy country, And slain thy people; The race of evil-doers shall nevermore be named.
21 A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
Prepare ye slaughter for his children, For the iniquity of their fathers, That they may no more arise, and possess the earth, And fill the world with enemies!”
22 “Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
For I will arise against them, saith Jehovah of hosts, And I will cut off from Babylon the name and remnant, Posterity and offspring, saith Jehovah.
23 “Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
I will make her the possession of the porcupine, and pools of water; Yea, I will sweep her away with the besom of destruction, saith Jehovah of hosts.
24 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
Jehovah of hosts hath sworn, saying, Surely, as I have devised, so shall it come to pass, The purpose which I have formed, that shall stand,
25 Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
To crush the Assyrian in my land, And to trample him on my mountains. Then shall his yoke depart from them, And his burden be removed from their shoulders.
26 Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
This is the purpose which is formed concerning all the earth, And this the hand which is stretched out over all the nations.
27 Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
For Jehovah of hosts hath decreed, and who shall disannul it? And his hand is stretched out, and who shall turn it back?
28 Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
In the year in which Ahaz the king died came this prophecy.
29 Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
Rejoice not, all Philistia, Because the rod that smote thee is broken, For from the root of a serpent shall come forth a basilisk, And his fruit shall be a flying, fiery serpent.
30 Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
Then shall the most wretched of the poor feed quietly, And the needy shall lie down in security; For I will kill thy root with famine, And thy remnant shall be slain.
31 Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
Howl, O gate! cry aloud, O city! O Philistia, thou meltest away in terror! For from the north cometh a smoke, And there is no straggler in their hosts.
32 Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”
What answer shall be given to the messengers of the nations? That Jehovah hath founded Zion, And in her shall the poor of his people find refuge.

< Ishaya 14 >