< Ishaya 14 >

1 Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
Thi Herren skal forbarme sig over Jakob og atter udvælge Israel og lade dem bosætte sig i deres Land; og den fremmede skal slutte sig til dem og holde sig til Jakobs Hus.
2 Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
Og Folkene skulle tage dem og føre dem til deres Hjem, og Israels Hus skal tage hine til Eje som Tjenere og Tjenestepiger i Herrens Land og holde dem fangne, som havde fanget dem selv, og regere over sine Undertrykkere.
3 A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
Og det skal ske paa den Dag, naar Herren skaffer dig Rolighed efter din Møje og din Uro og efter den haarde Trældom, med hvilken man lod dig trælle:
4 za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
Da skal du istemme denne Sang imod Kongen af Babel og sige: Hvorledes er Undertrykkeren hørt op! hvorledes er Trykket hørt op!
5 Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
Herren har sønderbrudt de ugudeliges Stav, Herskernes Spir,
6 wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
som slog Folkene i Grumhed med Slag uden Afladelse og regerede over Folkefærd i Vrede, med skaanselløs Forfølgelse.
7 Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
Al Jorden hviler og er stille, de raabe med frydefuldt Skrig.
8 Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
Cypresserne glæde sig ogsaa over dig, ja, Cedrene paa Libanon, og sige: Fra den Tid, du ligger, kommer ingen op at omhugge os.
9 Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
Dødsriget her neden til bæver for dig, for at møde dig, naar du kommer, det bringer Dødningerne til at rejse sig for din Skyld, alle Jordens mægtige, det lader alle Folkekongerne staa op fra deres Troner. (Sheol h7585)
10 Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
Alle svare de og sige til dig: Du er og bleven afmægtig som vi, du er bleven os lig!
11 An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
Din Højhed med dine Psaltres Brusen er nedkastet til Dødsriget; Orme bredes under dig, og Maddiker bedække dig. (Sheol h7585)
12 Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
Hvorledes er du falden ned fra Himmelen, du Morgenstjerne, du Morgenrødens Søn? hvorledes er du nedhugget til Jorden, du, som nedtraadte Folkefærd?
13 Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
Og du sagde i dit Hjerte: Jeg vil stige op til Himmelen, ophøje min Trone over Guds Stjerner, og jeg vil sidde paa Forsamlingsbjerget, yderst imod Norden;
14 Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
jeg vil fare op over de højeste Skyer, jeg vil være den Højeste lig!
15 Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
Men til Dødsriget skal du nedfare, til Hulens nederste Steder! (Sheol h7585)
16 Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
Hvo dig ser, skal stirre paa dig, de skulle betragte dig og sige: Mon denne være den Mand, som bragte Jorden til at bæve? som bragte Rigerne til at skælve?
17 mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
som gjorde Jorderige til en Ørk og nedbrød dets Stæder? som ikke løste sine bundne for at lade dem gaa hjem?
18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
Alle Folkenes Konger, de ligge alle med Ære, hver i sit Hus;
19 Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
men du, du er henslængt, uden Grav, som en vederstyggelig Kvist, bedækket med ihjelslagne, som ere gennemborede med Sværd, som fore ned i Stenhulens Dyb; du er som et nedtraadt Aadsel.
20 ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
Du skal ikke forenes med dem ved Begravelse; thi du har ødelagt dit Land, ihjelslaget dit Folk; de ondes Sæd skal ikke nævnes evindelig.
21 A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
Bereder hans Børn et Blodbad for deres Fædres Misgerning, at de ikke rejse sig, hverken til at arve Jorden eller til at fylde Jorderiges Kreds med Stæder.
22 “Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
Thi jeg vil staa op imod dem, siger den Herre Zebaoth, og udrydde Babels Navn og hans overblevne og Søn og Sønnesøn, siger Herren.
23 “Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
Og jeg vil gøre den til Bo for Pindsvin og til Vandsumpe og feje den bort med Ødelæggelsens Kost, siger den Herre Zebaoth.
24 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
Den Herre Zebaoth har svoret og sagt: Sandelig, som jeg har tænkt, skal det ske, og som jeg har besluttet, skal det staa fast:
25 Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
At jeg skal sønderknuse Assur i mit Land og nedtræde ham paa mine Bjerge, saa at hans Aag skal tages fra dem, og hans Byrde vige fra deres Skuldre!
26 Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
Dette er det Raad, som er besluttet over den hele Jord, og dette er den Haand, som er udrakt over alle Folkefærd.
27 Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
Thi den Herre Zebaoth har besluttet det, og hvo vil gøre det til intet? og hans Haand er udrakt, og hvo vil afvende den?
28 Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
I det Aar, der Kong Akas døde, skete denne Profeti.
29 Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
Glæd dig ikke, du ganske Filisterland! at hans Stav, som slog dig, er sønderbrudt; thi af Slangens Rod skal udgaa en Basilisk, og dens Frugt skal blive en flyvende Drage.
30 Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
Og de førstefødte af de ringe skulle finde Næring og de fattige ligge tryggelig; men jeg vil døde din Rod med Hunger, og man skal ihjelslaa de overblevne af dig.
31 Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
Hyl, Port! skrig, Stad! vær mistrøstig, du ganske Filisterland! thi der skal komme en Røg af Norden, og der er ingen Efternøler i hans Skarer.
32 Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”
Og hvad skal man svare Folkets Bud? — At Herren har grundfæstet Zion, og at de elendige af hans Folk skulle have Tilflugt i den.

< Ishaya 14 >