< Ishaya 13 >
1 Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
The birthun of Babiloyne, which birthun Ysaie, the sone of Amos, siy.
2 A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
Reise ye a signe on a myisti hil, and enhaunse ye vois; reise ye the hond, and duykis entre bi the yatis.
3 Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
Y haue comaundid to myn halewid men, and Y clepid my stronge men in my wraththe, that maken ful out ioie in my glorie.
4 Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
The vois of multitude in hillis, as of many puplis; the vois of sown of kyngis, of hethene men gaderit togidere. The Lord of oostis comaundide to the chyualry of batel,
5 Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
to men comynge fro a fer lond. The Lord cometh fro the hiynesse of heuene, and the vessels of his strong veniaunce, that he distrie al the lond.
6 Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
Yelle ye, for the dai of the Lord is niy; as wastyng it schal come of the Lord.
7 Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
For this thing alle hondis schulen be vnmyyti, and eche herte of man schal faile,
8 Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
and schal be al to-brokun. Gnawyngis and sorewis schulen holde Babiloyns; thei schulen haue sorewe, as they that trauelen of child. Ech man schal wondre at his neiybore; her cheris schulen be brent faces.
9 Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
Lo! the dai of the Lord schal come, cruel, and ful of indignacioun, and of wraththe, and of woodnesse; to sette the lond into wildirnesse, and to al to-breke the synneris therof fro that lond.
10 Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
For whi the sterris of heuene and the schynyng of tho schulen not sprede abrood her liyt; the sunne is maade derk in his risyng, and the moone schal not schine in hir liyt.
11 Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
And Y schal visite on the yuels of the world, and Y schal visite ayens wickid men the wickidnesse of hem; and Y schal make the pride of vnfeithful men for to reste, and Y schal make low the boost of stronge men.
12 Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
A man of ful age schal be preciousere than gold, and a man schal be preciousere than pure gold and schynyng.
13 Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
On this thing I schal disturble heuene, and the erthe schal be moued fro his place; for the indignacioun of the Lord of oostis, and for the dai of wraththe of his strong veniaunce.
14 Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
And it schal be as a doo fleynge, and as a scheep, and noon schal be that schal gadere togidere; ech man schal turne to his puple, and alle bi hem silf schulen fle to her lond.
15 Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
Ech man that is foundun, schal be slayn; and ech man that cometh aboue, schal falle doun bi swerd.
16 Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
The yonge children of them schulen be hurtlid doun bifore the iyen of them; her housis schulen be rauischid, and her wyues schulen be defoulid.
17 Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
Lo! Y schal reise on them Medeis, that seken not siluer, nethir wolen gold;
18 Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
but thei shulen sle litle children bi arowis, and thei schulen not haue merci on wombis yyuynge mylk, and the iye of them schal not spare on sones.
19 Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
And Babiloyne, thilke gloriouse citee in rewmes, noble in the pride of Caldeis, schal be destried, as God destried Sodom and Gomore.
20 Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
It shall not be enhabitid til in to the ende, and it schal not be foundid til to generacioun and generacioun; a man of Arabie schal not sette tentis there, and scheepherdis schulen not reste there.
21 Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
But wielde beestis schulen reste there, and the housis of hem schulen be fillid with dragouns; and ostrichis schulen dwelle there, and heeri beestis schulen skippe there.
22 Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.
And bitouris schulen answere there in the housis therof, and fliynge serpentis in the templis of lust.