< Ishaya 13 >

1 Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
[the] oracle of Babylon which he saw Isaiah [the] son of Amoz.
2 A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
On a mountain swept bare lift up a standard lift up a voice to them wave a hand so they may go [the] doors of noble [people].
3 Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
I I have commanded to consecrated [ones] my also I have summoned warriors my to anger my [the] exultant [ones] of pride my.
4 Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
[the] sound of A tumult [is] on the mountains [the] likeness of a people numerous [the] sound of an uproar of kingdoms of nations gathering Yahweh of hosts [is] mustering an army of battle.
5 Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
[they are] coming From a land of distance from [the] end of the heavens Yahweh and [the] weapons of indignation his to destroy all the land.
6 Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
Wail for [is] near [the] day of Yahweh like devastation from [the] Almighty it will come.
7 Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
There-fore all hands they will drop and every heart of a person it will melt.
8 Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
And they will be terrified - pangs and pains they will seize [them]! like [woman] giving birth they will be in anguish! each to neighbor his they will look in astonishment [will be] faces of flames faces their.
9 Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
There! [the] day of Yahweh [is] coming a cruel [day] and wrath and burning of anger to make the land a waste and sinners its he will destroy from it.
10 Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
For [the] stars of the heavens and constellations their not they will flash forth light their it will be dark the sun when goes forth it and [the] moon not it will make shine light its.
11 Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
And I will visit on [the] world evil and on wicked [people] iniquity their and I will put an end to [the] pride of arrogant [people] and [the] haughtiness of ruthless [people] I will bring low.
12 Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
I will make precious humankind more than pure gold and humankind more than [the] gold of Ophir.
13 Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
There-fore heaven I will make tremble and it may shake the earth from place its in [the] wrath of Yahweh of hosts and in [the] day of [the] burning of anger his.
14 Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
And it will be like a gazelle hunted and like sheep and there not [will be one who] gathers everyone to own people his they will turn and everyone to own land his they will flee.
15 Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
Every [one who] is found he will be pierced through and every [one who] is captured he will fall by the sword.
16 Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
And children their they will be dashed in pieces to eyes their they will be plundered houses their and wives their (they will be lain with. *Q(K)*)
17 Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
Here I [am] about to rouse on them Media who silver not they value and gold not they delight in it.
18 Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
And bows youths they will dash in pieces and [the] fruit of [the] womb not they will have compassion on on children not it will look with pity eye their.
19 Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
And it will be Babylon [the] beauty of kingdoms [the] splendor of [the] pride of [the] Chaldeans like [the] overthrow of God Sodom and Gomorrah.
20 Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
Not it will remain to perpetuity and not it will settle until a generation and a generation and not he will pitch a tent there an Arab and shepherds not they will make lie down there.
21 Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
And they will lie down there desert-dwellers and they will be full houses their jackals and they will dwell there daughters of an ostrich and goats they will leap about there.
22 Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.
And it will sing hyenas in palaces its and jackals in [the] palaces of delight and [is] near to go time its and days its not they will be prolonged.

< Ishaya 13 >