< Ishaya 13 >
1 Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
THE VISION WHICH ESAIAS SON OF AMOS SAW AGAINST BABYLON.
2 A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
Lift up a standard on the mountain of the plain, exalt the voice to them, beckon with the hand, open [the gates], you rulers.
3 Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
I give command, and I bring them: giants are coming to fulfil my wrath, rejoicing at the same time and insulting.
4 Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
A voice of many nations on the mountains, [even] like [to that] of many nations; a voice of kings and nations gathered together: the Lord of hosts has given command to a warlike nation,
5 Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
to come from a land afar off, from the utmost foundation of heaven; the Lord and his warriors [are coming] to destroy all the world.
6 Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
Howl you, for the day of the Lord is near, and destruction from God shall arrive.
7 Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
Therefore every hand shall become powerless, and every soul of man shall be dismayed.
8 Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
The elders shall be troubled, and pangs shall seize them, as of a woman in travail: and they shall mourn one to another, and shall be amazed, and shall change their countenance as a flame.
9 Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
For behold! the day of the Lord is coming which can’t be escaped, [a day] of wrath and anger, to make the world desolate, and to destroy sinners out of it.
10 Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
For the stars of heaven, and Orion, and all the host of heaven, shall not give their light; and it shall be dark at sunrise, and the moon shall not give her light.
11 Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
And I will command evils for the whole world, and [will visit] their sins on the ungodly: and I will destroy the pride of transgressors, and will bring low the pride of the haughty.
12 Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
And they that are left shall be more precious than gold tried in the fire; and a man shall be more precious than the stone that is in Suphir.
13 Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
For the heaven shall be enraged, and the earth shall be shaken from her foundation, because of the fierce anger of the Lord of hosts, in the day in which his wrath shall come on.
14 Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
And they that are left shall be as a fleeing fawn, and as a stray sheep, and there shall be none to gather [them]: so that a man shall turn back to his people, and a man shall flee to his own land.
15 Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
For whoever shall be taken shall be overcome; and they that are gathered together shall fall by the sword.
16 Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
And they shall dash their children before their eyes; and they shall spoil their houses, and shall take their wives.
17 Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
Behold, I will stir up against you the Medes, who do not regard silver, neither have they need of gold.
18 Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
They shall break the bows of the young men; and they shall have no mercy on your children; nor shall their eyes spare your children.
19 Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
And Babylon, which is called glorious by the king of the Chaldeans, shall be as [when] God overthrew Sodoma, and Gomorrha.
20 Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
It shall never be inhabited, neither shall any enter into it for many generations: neither shall the Arabians pass through it; nor shall shepherds at all rest in it.
21 Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
But wild beasts shall rest there; and the houses shall be filled with howling; and monsters shall rest there, and devils shall dance there, and satyrs shall dwell there; and hedgehogs shall make their nests in their houses. It will come soon, and will not wait.
22 Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.