< Ishaya 13 >

1 Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
Břímě Babylona, kteréž viděl Izaiáš syn Amosův.
2 A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
Na hoře vysoké vyzdvihněte korouhev, povyšte hlasu k nim, dejte návěští rukou, ať vejdou do bran knížecích.
3 Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
Já jsem přikázal posvěceným svým, povolal jsem také i udatných reků svých k vykonání hněvu svého, veselících se z vyvýšení mého.
4 Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
Hlas množství na horách, jakožto lidu mnohého, hlas a zvuk království a národů shromážděných: Hospodin zástupů sbírá vojsko k válce.
5 Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
Táhnou z země daleké od končin nebes. Hospodin a osudí prchlivosti jeho, aby poplénil všecku zemi.
6 Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
Kvělte, nebo blízko jest den Hospodinův, jako zpuštění od Všemohoucího přijde.
7 Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
A protož všeliké ruce oslábnou, a všeliké srdce člověka rozplyne se.
8 Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
I budou předěšeni, svírání a bolesti je zachvátí, jako rodička stonati budou; každý nad bližním svým užasne se, tváře jejich k plameni podobné budou.
9 Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
Aj, den Hospodinův přichází přísný, a zůřivost a rozpálení hněvu, aby obrátil tu zemi v poušť, a hříšníky její z ní vyhladil.
10 Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
Nebo hvězdy nebeské a planéty jejich nedopustí svítiti světlu svému; zatmí se slunce při vycházení svém, a měsíc nevydá světla svého.
11 Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
A navštívím na okršlku země zlost, a na bezbožných nepravost jejich; a káži přestati pýše pyšných, a vysokomyslnost tyranů snížím.
12 Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
Způsobím to, že dražší bude člověk nad zlato čisté, člověk, pravím, nad zlato z Ofir.
13 Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
Z té příčiny zatřesu nebesy, a pohne se země z místa svého, v prchlivosti Hospodina zástupů, a ve dni rozpálení hněvu jeho.
14 Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
I bude jako srna zplašená, a jako stádo, když není, kdo by je shromáždil; jeden každý k lidu svému se obrátí, a každý do země své uteče.
15 Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
Kdožkoli nalezen bude, bude proboden, a kteříž by se koli shlukli, od meče padnou.
16 Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
Nadto i dítky jejich rozrážíny budou před očima jejich, domové jejich zloupeni, a ženy jejich poškvrněny.
17 Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
Aj, já vzbudím proti nim Médské, kteříž sobě stříbra nebudou vážiti, a v zlatě nebudou se kochati,
18 Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
Ale z luků dítky rozrážeti, aniž se nad plodem života slitují, aniž synům odpustí oko jejich.
19 Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
I budeť Babylon, někdy ozdoba království a okrasa důstojnosti Kaldejské, podobný podvrácené Sodomě a Gomoře.
20 Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
Nebudou se v něm osazovati na věky, ani bydliti od pokolení až do pokolení; aniž rozbije tam stanu svého Arab, ani pastýři tam odpočívati budou.
21 Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
Ale lítá zvěř tam odpočívati bude, a domové jejich šelmami naplněni budou; bydliti budou tam i sovy, a příšery tam skákati budou.
22 Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.
Ozývati se také budou sobě hrozné potvory na palácích jejich, a draci na hradích rozkošných. A blízkoť jest, že přijde čas jeho, a dnové jeho prodlévati nebudou.

< Ishaya 13 >