< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
І ти скажеш дня того: Хвалю́ Тебе, Господи, бо Ти гні́вавсь на мене, та гнів Твій вщуха́є, й мене Ти пора́дуєш,
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
оце, — Бог спасі́ння моє! Безпечний я, і не боюсь, бо Госпо́дь, — Господь сила моя та мій спів, і спасі́нням для мене Він став!
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
І ви в радості бу́дете че́рпати воду з спасе́нних джере́л!
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
І скажете ви того дня: „Дя́куйте Господу, кличте Іме́ння Його́, сповісті́ть між наро́дів про вчинки Його, пригадайте, що Йме́ння Його превеличне!
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
Співайте для Господа, Він бо вели́чне вчинив, і хай це́ буде зна́не по ці́лій землі!
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Радій та співай, ти мешка́нко Сіону, бо серед тебе Великий, — Святий Ізраїлів!

< Ishaya 12 >