< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
İsrail halkı o gün, “Ya RAB, sana şükrederiz” diyecek, “Bize öfkelenmiştin ama öfken dindi, Bizi avuttun.
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
Tanrı kurtuluşumuzdur. O'na güvenecek, yılmayacağız. Çünkü RAB gücümüz ve ezgimizdir. O kurtardı bizi.”
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
Kurtuluş pınarlarından sevinçle su alacaksınız.
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
O gün diyeceksiniz ki, “RAB'be şükredin, O'nu adıyla çağırın, Halklara duyurun yaptıklarını, Adının yüce olduğunu duyurun!
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
RAB'be ezgiler söyleyin, Çünkü görkemli işler yaptı. Bütün dünya bilsin bunu.
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Ey Siyon halkı, sesini yükselt, sevinçle haykır! Çünkü aranızda bulunan İsrail'in Kutsalı büyüktür.”

< Ishaya 12 >