< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
Et tu diras en ce jour-là; Eternel! je te célébrerai, parce qu'ayant été courroucé contre moi, ta colère s'est apaisée, et tu m'as consolé.
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
Voici, le [Dieu] Fort est ma délivrance, j'aurai confiance, et je ne serai point effrayé; car l'Eternel, l'Eternel [est] ma force et ma louange, et il a été mon Sauveur.
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
Et vous puiserez des fontaines de cette délivrance des eaux avec joie.
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
Et vous direz en ce jour-là; Célébrez l'Eternel, réclamez son Nom, faites connaître parmi les peuples ses exploits, faites souvenir que son Nom est une haute retraite.
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
Psalmodiez à l'Eternel, car il a fait des choses magnifiques; cela est connu dans toute la terre.
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Habitante de Sion, égaye-toi, et te réjouis avec chant de triomphe; car le Saint d'Israël est grand au milieu de toi.

< Ishaya 12 >