< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
Et tu diras en ce jour-là: Je te loue, Yahweh, car tu étais irrité, mais ta colère s’est détournée et tu me consoles.
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
Voici le Dieu de ma délivrance; j’ai confiance et je ne crains pas; car ma force et ma louange c’est Yahweh, Yahweh; il a été pour moi le salut. —
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
Vous puiserez des eaux avec joie aux sources du salut,
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
et vous direz en ce jour-là: Louez Yahweh, invoquez son nom, publiez parmi les peuples ses grandes œuvres, proclamez que son nom est élevé.
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
Chantez Yahweh, car il a fait des choses magnifiques; qu’on le sache dans toute la terre!
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Pousse des cris, tressaille d’allégresse, habitante de Sion, car le Saint d’Israël est grand au milieu de toi!

< Ishaya 12 >