< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
Silloin pitää sinun sanoman: minä kiitän sinua, Herra, ettäs vihainen olet ollut minun päälleni; mutta sinun vihas on palannut, ja sinä lohdutat minua.
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
Katso, Jumala on minun autuuteni, minä olen turvassa ja en mitään pelkää; sillä Herra, Herra on minun väkevyyteni, ja minun virteni, ja hän on minun autuuteni.
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
Teidän pitää ammuntaman vettä ilolla autuuden lähteistä.
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
Ja silloin te sanotte: kiittäkäät Herraa, ja saarnatkaat hänen nimeänsä, julistakaat kansoissa hänen tekojansa, muistakaat kuinka korkia hänen nimensä on.
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
Veisatkaat kiitosta Herralle, sillä hän on voimallisesti itsensä asettanut; se olkoon tiettävä kaikessa maassa.
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Korota äänes ja veisaa, sinä Zionin asuvainen, sillä Israelin pyhä on suuri sinun keskelläs.

< Ishaya 12 >