< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
And you will say in the day that I will give thanks you O Yahweh for you were angry with me let it turn back anger your and may you comfort me.
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
Here! God [is] salvation my I will trust and not I will be in dread for [is] might my and strength Yahweh Yahweh and he has become of me salvation.
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
And you will draw water with joy from [the] springs of salvation.
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
And you will say in the day that give thanks to Yahweh call on name his make known among the peoples deeds his bring to remembrance that [is] exalted name his.
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
Sing praises to Yahweh for majesty he has done ([is] made known *Q(K)*) this in all the earth.
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Cry aloud and cry out O inhabitant[s] of Zion for [is] great in midst your [the] holy [one] of Israel.

< Ishaya 12 >