< Ishaya 12 >

1 A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
And you have said in that day: “I thank you, O YHWH, Though You have been angry with me, Your anger turns back, And You comfort me.
2 Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
Behold, God [is] my salvation, I trust, and do not fear, For my strength and song [is] YAH—YHWH, And He is to me for salvation.
3 Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
And you have drawn waters with joy Out of the fountains of salvation,
4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
And you have said in that day, Give praise to YHWH, call on His Name. Make His acts known among the peoples. Make mention that His Name is set on high.
5 Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
Praise YHWH, for He has done excellence, This is known in all the earth.
6 Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”
Cry aloud, and sing, O inhabitant of Zion, For the Holy One of Israel [is] great in your midst!”

< Ishaya 12 >