< Ishaya 11 >
1 Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
Och ett Ris skall uppgå, utaf Isai slägte, och en Telning utaf hans rot frukt bära;
2 Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
På hvilkom skall hvilas Herrans Ande, vishets och förstånds ande, råds och starkhets ande, kunskaps och Herrans fruktans ande.
3 zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
Han skall inblåsa honom Herrans fruktan, att han icke skall döma efter som ögonen se, eller straffa efter som öronen höra;
4 amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
Utan skall med rättviso döma de fattiga, och med dom straffa de elända på jordene, och skall slå jordena med sins muns staf, och med sina läppars anda dräpa de ogudaktiga.
5 Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
Rättvisa skall vara hans länders bälte, och trohet hans njurars bälte.
6 Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
Ulfvar skola bo tillsammans med lamb, och parder ligga ibland kid; en liten dräng skall tillhopa drifva kalfvar, och ung lejon, och gödeboskap.
7 Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
Kor och björnar skola gå i bet, och deras ungar tillhopa ligga, och lejonen skola äta halm, såsom oxar;
8 Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
Och ett spenabarn skall lust hafva vid en huggorms hål, och ett afvandt barn skall stinga sina hand uti ena basiliskes kulo.
9 Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
Man skall ingen sarga eller förderfva på mitt helga berg; ty landet är fullt af Herrans kunskap, lika som med hafsens vatten betäckt.
10 A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
Och det skall ske på den tiden, att Isai rot, som står till folks baner, der skola Hedningarna fråga efter, och hans hvila skall vara ära.
11 A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
Och Herren skall på den tiden än en gång uträcka sina hand, att han skall få det återlefda af sitt folk, det qvart blifvet är för de Assyrier, Egyptier, Pathros, Ethioper, Elamiter, Sinear, Hamath, och för hafsens öar;
12 Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
Och skall uppresa ett baner ibland Hedningarna, och sammanhemta de fördrefna af Israel, och församla de förskingrada af Juda, af fyra jordenes ändar.
13 Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
Och det nit emot Ephraim skall återvända, och Juda fiender skola utrotade varda, så att Ephraim icke hatar Juda, och Juda icke skall vara emot Ephraim.
14 Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
Men de skola vara de Philisteer på halsen vesterut, och beröfva alla de som österut bo; Edom och Moab skola gå dem tillhanda; Ammons barn skola hörsam vara.
15 Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
Och Herren skall tillspillogifva hafsens ström uti Egypten, och skall låta gå sina hand öfver älfvena med starkt väder, och slå de sju strömmar, så att man må gå torrskodd deröfver;
16 Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.
Och skall vara dem qvarlefdom af sitt folk, som igenblifvet är för de Assyrier, en väg; såsom Israel skedde på den tiden, de utur Egypti land drogo.