< Ishaya 11 >
1 Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
Y saldrá un retoño del tronco de Isaí, y una rama de sus raíces dará fruto.
2 Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
Y el espíritu del Señor descansará sobre él, el espíritu de sabiduría e inteligencia, el espíritu de guía sabia y poder, el espíritu de conocimiento y del temor del Señor;
3 zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
Y le hará entender diligentemente el temor del Señor, no será guiado en su juicio por lo que ve, ni tomará decisiones por lo que oigan sus oídos;
4 amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
Pero él hará lo correcto en la causa de los pobres y tomará decisiones sabias para aquellos en la tierra que están en necesidad; y la vara de su boca caerá sobre el cruel, y con el soplo de sus labios pondrá fin al malvado.
5 Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
Y la justicia será el cordón de su túnica, y fidelidad la banda que rodea su pecho.
6 Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
Y el lobo vivirá con el cordero, y el leopardo tomará su descanso con el cabrito; y el leoncillo tomará hierba para comer con él becerro; y un niño pequeño será su guía.
7 Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
Y la vaca y la osa serán amigos mientras sus pequeños duermen juntos.
8 Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
Y el niño de pecho jugará por el agujero de la serpiente, y el niño mayor pondrá su mano en la grieta de la serpiente venenosa.
9 Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
No habrá causa de dolor ni destrucción en toda mi montaña sagrada: porque la tierra estará llena del conocimiento del Señor así como el mar está cubierto por las aguas.
10 A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
Y en ese día, los ojos de las naciones se volverán a la raíz de Isaí, que se alzará como la bandera de los pueblos; y su lugar de descanso será la gloria.
11 A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
Y en ese día, la mano del Señor se extenderá por segunda vez para recuperar al resto de su pueblo, desde Asiria y desde Egipto, y desde Patros, y desde Etiopía, y desde Elam, y desde Sinar, y de Hamat, y de las tierras marinas.
12 Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
Y pondrá una bandera como señal a las naciones, y reunirá a los de Israel que habían sido enviados, y a los errantes de Judá, de los cuatro extremos de la tierra.
13 Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
Y la envidia de Efraín desaparecerá, y los que causan problemas a Judá se acabarán; Efraín ya no tendrá más envidia de Judá, y se acabará el odio de Judá por Efraín.
14 Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
Y se unirán para atacar a los filisteos en el oeste, y juntos tomarán los bienes de los hijos del este, su mano estará sobre Edom y Moab; y los hijos de Amón estarán bajo su gobierno.
15 Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
Y el Señor secará completamente la lengua del mar egipcio; y con su viento ardiente, su mano se extenderá sobre el río, y se dividirá en siete arroyos, para que los hombres puedan cruzarlo con sandalias en seco.
16 Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.
Habrá un camino para el resto de su pueblo desde Asiria; como lo hubo para Israel el día en que salió de la tierra de Egipto.