< Ishaya 11 >

1 Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
Then shall spring forth a shoot from the stem of Jesse, And a sprout grow up from his roots.
2 Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
The spirit of Jehovah shall rest upon him, The spirit of wisdom and understanding, The spirit of counsel and might, The spirit of the knowledge and of the fear of Jehovah,
3 zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
He shall take delight in the fear of Jehovah; He shall not judge by the sight of his eyes, Nor decide by the hearing of his ears.
4 amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
But with righteousness shall he judge the poor, And decide with equity for the afflicted of the land; He shall smite the earth with the rod of his mouth; With the breath of his lips shall he slay the wicked.
5 Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
Righteousness shall be the girdle of his loins, And faithfulness the girdle of his reins.
6 Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
Then shall the wolf dwell with the lamb, And the leopard shall lie down with the kid; The calf, and the young lion, and the fatling shall be together, And a little child shall lead them.
7 Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
The cow and the bear shall feed together, Together shall their young lie down, And the lion shall eat straw like the ox.
8 Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
The suckling shall play upon the hole of the asp, And the near-weaned child lay his hand on the hiding-place of the basilisk.
9 Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
They shall not hurt nor destroy in all my holy mountain; For the land shall be full of the knowledge of Jehovah, As the waters cover the depths of the sea.
10 A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
In that day shall the shoot of Jesse stand as a banner to the nations, And to him shall the gentiles repair, And his dwelling-place shall be glorious.
11 A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
In that day shall Jehovah the second time stretch forth his hand To recover the remnant of his people, That remaineth, from Assyria, and from Egypt, And from Pathros, and from Ethiopia, and from Elam, And from Shinar, and from Hamath, And from the islands of the sea.
12 Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
He shall set up a banner to the nations, And gather the outcasts of Israel, And bring together the dispersed of Judah, From the four extremities of the earth.
13 Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
Then shall the jealousy of Ephraim depart, And the enmity in Judah be at an end; Ephraim shall not be jealous of Judah, And Judah shall not contend with Ephraim.
14 Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
But they shall fly upon the shoulders of the Philistines at the sea; Together shall they plunder the children of the East; On Edom and Moab shall they lay their hand, And the sons of Ammon shall be subject to them.
15 Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
Then will Jehovah utterly destroy the tongue of the Egyptian sea, And shake his hand over the river with a mighty wind, And smite it into seven streams, So that men may go over it dry-shod.
16 Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.
And it shall be a highway for the remnant of the people, Which shall remain, from Assyria, As there was to Israel, When he came up from the land of Egypt.

< Ishaya 11 >