< Ishaya 11 >

1 Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
And a Rod has come out from the stock of Jesse, And a Branch is fruitful from his roots.
2 Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
The Spirit of YHWH has rested on Him, The Spirit of wisdom and understanding, The Spirit of counsel and might, The Spirit of knowledge and fear of YHWH.
3 zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
To refresh Him in the fear of YHWH, And He does not judge by the sight of His eyes, Nor decides by the hearing of His ears.
4 amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
And He has judged the poor in righteousness, And decided for the humble of earth in uprightness, And has struck earth with the rod of His mouth, And He puts the wicked to death with the breath of His lips.
5 Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
And righteousness has been the girdle of His loins, And faithfulness—the girdle of His reins.
6 Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
“And a wolf has sojourned with a lamb, And a leopard lies down with a kid, And calf, and young lion, and fatling [are] together, And a little youth is leader over them.
7 Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
And cow and bear feed, Together their young ones lie down, And a lion eats straw as an ox.
8 Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
And a suckling has played by the hole of a cobra, And on the den of a viper The weaned one has put his hand.
9 Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
They do no evil, nor destroy in all My holy mountain, For the earth has been full with the knowledge of YHWH, As the waters are covering the sea.”
10 A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
And there has been, in that day, A Root of Jesse that is standing for an ensign of peoples, Nations seek Him, And His rest has been glorious!
11 A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
And it has come to pass in that day, The Lord adds His power a second time, To get the remnant of His people that is left, From Asshur, and from Egypt, And from Pathros, and from Cush, And from Elam, and from Shinar, And from Hamath, and from islands of the sea,
12 Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
And He has lifted up an ensign to nations, And gathers the driven away of Israel, And He assembles the scattered of Judah, From the four wings of the earth.
13 Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
And has turned aside the envy of Ephraim, And the adversaries of Judah are cut off, Ephraim does not envy Judah, And Judah does not distress Ephraim.
14 Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
And they have flown on the shoulder of the Philistines westward, Together they spoil the sons of the east, Edom and Moab sending forth their hand, And sons of Ammon obeying them.
15 Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
And YHWH has devoted to destruction The tongue of the Sea of Egypt, And has waved His hand over the river, In the terror of His wind, And has struck it at the seven streams, And has caused [men] to tread [it] with shoes.
16 Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.
And there has been a highway, For the remnant of His people that is left, from Asshur, As there was for Israel in the day of his coming up out of the land of Egypt!

< Ishaya 11 >