< Ishaya 10 >

1 Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
A UWE ka poe kau i na kanawai hewa, A me ka poe kakauolelo, i kakau i na mea kekee;
2 don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
I kipaku i ka poe kaumaha, mai ka hooponoia'ku, A kaili aku hoi i ka pono o ko'u poe kanaka poino, I pio ia lakou na wahinekanemake, A hao wale hoi i na keiki makua ole!
3 Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
Pehea la oukou e hana'i i ka la o ka hoopui ana, Ke hiki mai ka make mai kahi loihi mai? Ia wai oukou e holo ai no ke kokuaia mai? Mahea oukou e waiho ai i ko oukou waiwai?
4 Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
I haaleleia e au, e kulou no lakou malalo me na mea pio, A e hina hoi malalo me na mea i lukuia. Aole nae i huli aku kona huhu no keia mau mea a pau, Aka, ke o mai nei no kona lima i keia manawa.
5 “Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
Auwe ko Asuria! ka laau hahau o kuu ukiuki, A o ua laau hahau la, aia no ia ma ko lakou lima, Oia hoi kuu inaina.
6 Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
E hoouna aku au ia ia, e ku e i ka lahuikanaka aia, E kauoha aku no wau ia ia, E ku e i ka poe kanaka a'u i huhu ai; E hao aku i ka waiwaipio, a e lawe aku hoi i ka mea i paa; A e hahi ia lakou ilalo, e like me ka lepo o ke alanui.
7 Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
Aole pela kona manao, Aole i noonoo kona naau pela; O ka luku no ka mea iloko o kona naau, A e anai aku i na aina he nui loa.
8 Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
I mai la ia, aole anei he poe alii nui ko'u poe alii?
9 ‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
Aole anei i like o Kaleno me Karekemisa? A o Hamata hoi me Arepada? A o Samaria me Damaseko?
10 Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
E like me ka loaa i kuu lima na aupuni o na'kua kii, Ua oi aku ko lakou akua kii mamua o ko Ierusalema, A mamua hoi o ko Samaria;
11 ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
Me au i hana aku ai ia Samaria a me kona poe akua kii, Aole anei au e hana pela ia Ierusalema a me kona mau akua?
12 Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
A hiki aku i ka wa, e hooki ai ka Haku i kana hana a pau, Maluna o ka mauna o Ziona, a me Ierusalema, Alaila wau e hoopai aku ai i ka hua o ka naau kiekie o ke alii o Asuria, A me ka hookano ana o kona maka hookiekie.
13 Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
No ka mea, ua olelo mai ia, Ua hana au i keia, i ka ikaika o ko'u lima iho, A i kuu akamai hoi, no ka mea, ua maalea au. Na'u no i hooneenee i na mokuna o na aina, A ua hao aku au i ko lakou waiwai, A e like hoi me ke kanaka koa, ua hoohaahaa wau i ka poe e noho ana.
14 Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
Me he punana la i loaa'i i kuu lima ka waiwai o na lakuikanaka; A e like me ka hoiliili ana o na hua manu i haaleleia, Pela no wau i hoiliili ai i ko na aina a pau; Aohe mea i upoi ka eheu, Aohe mea i hamama ka waha a ioio.
15 Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
E hookiekie anei ke koilipi maluna o ka mea nana e kalai me ia? E haanui anei ka pahiolo maluna o ka mea nana ia e oloolo? Me he laau la i wiliwili i kona mea nana e hapai, E like me ke kookoo hoi i hoala ia ia iho me he mea laau ole la.
16 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
Nolaila e hoouna mai ai ka Haku, ka Haku o na kaua, I ka wiwi maluna o kona poe puipui; A malalo iho o kona nani e puhi ai oia i ka mea aa, E like me ke aa ana o ke ahi.
17 Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
E lilo no ka malamalama o Iseraela i ahi, A o kona Mea Hemolele hoi i lapalapa ahi; A e puhi no ia, a e hoopau ma ka la hookahi, I kona nahele ooi, a me kona laau kalakala.
18 Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
E hoopau loa no ia i ka nani o kona ululaau, A me ka mahinaai hua nui, mai ka uhane a ke kino; A e like auanei ia me ka mea mai hokii loa.
19 Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
E uuku ana no ke koena o kona ululaau, E hiki no i ke keiki uuku ke palapala ia lakou.
20 A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
A hiki aku i kela la, O ke koena o ka Iseraela, O ka poe hoi i pakele o ka ohana a Iakoba, Aole lakou e hilinai hou maluna o ka mea nana lakou i pepehi; Aka, e hilinai io no maluna o Iehova, A maluna hoi o ka Mea Hemolele o ka Iseraela.
21 Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
He koena no ke hoi mai, he koena no Iakoba, I ke Akua mana loa.
22 Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
Ina paha i like kou poe kanaka o Iseraela, Me ke one o ke kai, He koena wale no o lakou ke hoi mai; Ua holo ka olelo no ka hoopau ana, E hiki wawe mai ia, me ka pololei hoi.
23 Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
He oiaio no, ua holo ka olelo no ka hoopau ana, A na ka Haku no, na Iehova o na kaua e hana mai, Mawaena konu o ka aina a pau.
24 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
Nolaila i olelo mai ai ka Haku, o Iehova o na kaua, peneia, E ko'u poe kanaka e noho la ma Ziona, Mai makau oukou i ko Asuria; E hahau mai no lakou me ka laau hahau, A e hapai no hoi i ke kookoo maluna ou, E like me ka hana ana o Aigupita.
25 Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
Aka, he wahi manawa uuku no e koe, Alaila, e kaa no kuu inaina, a me ko'u ukiuki hoi. Ma ke anaiia'ku o lakou.
26 Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
Na Iehova o na kaua e hapai i laau hahau maluna o lakou, E like me ka hahau ana i ko Midiana ma ka pohaka o Oreba: A me ka laau ana i hapai ai maluna o ke kai, E hapai no oia ia e like me kana hana ana i ko Aigupita.
27 A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
A hiki mai ia la, E laweia'ka kona mea kanmaha, mai koa poohiwi ako, A me kona auamo maluna ako o kou a-i, E hakiia auanei imua o ka mea puipui
28 Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
Ua hele mai ia i Aiata, ua hala loa aku i Migerona, Ua waiho no i kana ukana ma Mikemasa:
29 Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
Ua hele mai lakou ma keia aoao o ke ahua; Aia ma Geba ko lakou wahi moe i ka po: Ua makau ko Rama; ua holo ko Gibea Saula.
30 Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
E hookiekie i koa leo, e ke kaikamahine a Galima; E hoolohe oe, e Laisa; Auwe Anatota poino!
31 Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
Ua holo o Mademena: Ua hee ka poe i noho ma Gebima.
32 A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
Hookahi no la e koe o kona noho ana ma Noba, A e lulu ia i kona lima e ku e i ka mauna o ke kaikamahine o Ziona, I ka puu hoi o Ierusalema.
33 Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
Aia hoi, na ka Haku, na Iehova o na kaua, E okioki i na lala me ka weliweli, A e kuaia ilalo na mea kiekie loa, A e hoohaahaaia na mea hookano.
34 Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.
E kuaia ilalo me ka hao i na ululaau paapu, A e haule hoi o Lebanona imua o ka mea mana.

< Ishaya 10 >