< Ishaya 10 >

1 Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
Malheur à ceux qui établissent des lois iniques, et qui écrivant, ont écrit l’injustice;
2 don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
Afin d’opprimer le pauvre dans le jugement, et de faire violence à la cause des faibles de mon peuple; afin que les veuves soient leur proie, et qu’ils pillent les orphelins!
3 Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
Que ferez-vous au jour de la visite et de la calamité, venant de loin? De qui solliciterez-vous le secours, et où abandonnerez-vous votre gloire,
4 Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Pour n’être point courbés sous la chaîne, et ne point tomber avec les tués? Après toutes ces choses sa fureur n’a pas été détournée, mais sa main est encore étendue.
5 “Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
Malheur à Assur! la verge et le bâton de ma fureur, c’est lui; dans sa main est mon indignation.
6 Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
Je l’enverrai vers une nation trompeuse, je lui donnerai des ordres contre le peuple de ma fureur, afin qu’il emporte des dépouilles, et qu’il enlève du butin, et qu’il le foule aux pieds comme la boue des places publiques.
7 Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
Mais lui-même ne pensera pas ainsi, et son cœur n’aura pas un pareil sentiment; mais son cœur sera porté à la destruction et à la ruine totale d’un grand nombre de nations.
8 Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
Car il dira:
9 ‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
Est-ce que mes princes ne sont pas autant de rois? Est-ce que Calano n’est pas comme Charcamis; et Emath comme Arphad? est-ce que Samarie n’est pas comme Damas?
10 Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
De même que ma main a atteint les royaumes des idoles, de même aussi j’atteindrai les simulacres de Jérusalem et de Samarie.
11 ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
Est-ce que comme j’ai fait à Samarie et à ses idoles, je ne ferai pas à Jérusalem et à ses simulacres?
12 Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
Et il arrivera que, lorsque le Seigneur aura accompli toutes ses œuvres sur la montagne de Sion et dans Jérusalem, je visiterai le fruit du cœur arrogant du roi d’Assur, et la fierté de ses yeux altiers.
13 Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
Car il a dit: Par la force de ma main j’ai fait, par ma sagesse j’ai compris; et j’ai arraché les limites des peuples, et j’ai spolié les princes, et comme puissant j’ai fait descendre ceux qui étaient assis sur un trône élevé.
14 Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
Et ma main a atteint comme un nid la puissance des nations; et de même qu’on recueille des œufs qui ont été abandonnés, de même moi j’ai réuni toute la terre; et il ne s’est trouvé personne qui remuât l’aile et ouvrit la bouche, et fit entendre le moindre cri.
15 Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
Est-ce que la hache se glorifiera contre celui qui s’en sert pour fendre? ou la scie s’élèvera-t-elle contre celui par qui elle est mise en mouvement? C’est comme si la verge s’élevait contre celui qui la lève; et comme si le bâton se glorifiait, lui qui est absolument du bois.
16 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
À cause de cela le dominateur. Seigneur des armées, enverra la maigreur au milieu de ses gras: et au-dessous de sa gloire s’allumera et s’enflammera comme un brasier ardent.
17 Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
Et la lumière d’Israël sera le feu, et son Saint la flamme; et les épines et les ronces d’Assur s’embraseront et seront dévorées dans un seul jour.
18 Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
Et la gloire de sa forêt et de son Carmel, depuis l’âme jusqu’à la chair, sera {consumée; et Assur de frayeur s’enfuira.
19 Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
Et les restes des arbres de sa forêt, à cause de leur petit nombre, se compteront aisément, et un enfant pourra les enregistrer.
20 A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Et il arrivera en ce jour-là que le reste d’Israël et ceux qui auront échappé de la maison de Jacob, ne s’appuieront plus sur celui qui les frappe, mais ils s’appuieront avec sincérité sur le Seigneur, le saint d’Israël.
21 Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
Les restes se convertiront (les restes de Jacob, dis-je) au Dieu fort.
22 Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
Car lors-même que ton peuple, ô Israël, serait comme le sable de la mer, les restes seulement se convertiront; ces restes, réduits à un petit nombre, abonderont en justice.
23 Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
Car le Seigneur Dieu des armées fera une destruction et un retranchement au milieu de toute la terre.
24 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu des armées: Mon peuple, habitant de Sion, ne crains pas Assur; avec la verge il te frappera, et il lèvera son bâton sur toi, dans la voie de l’Egypte,
25 Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
Car encore un peu, et un moment, et mon indignation et ma fureur seront à leur comble à cause de leur crime.
26 Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
Et le Seigneur des armées lèvera sur lui le fouet, comme il frappa Madian à la pierre d’Oreb, et sa verge sur la mer, et il la lèvera dans la voie de l’Egypte.
27 A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
Et il arrivera en ce jour-là, que le fardeau d’Assur sera ôté de ton épaule, et son joug de ton cou; et le joug pourrira à cause de l’huile.
28 Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
Il viendra à Aïath, il passera par Magron; à Machmas il déposera ses bagages.
29 Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
Ils ont passé en courant Gaba, notre campement; Rama a été frappé de stupeur, Gabaath de Saül a pris la fuite.
30 Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
Fais retentir la voix, fille de Gallim: sois attentive, Laïsa et toi aussi, pauvre Anathoth.
31 Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
Médéména a émigré: habitants de Gabim, rassurez-vous.
32 A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
Il est encore jour pour s’arrêter à Nobé; il agitera sa main contre la montagne de la fille de Sion, et la colline de Jérusalem.
33 Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
Voici que le dominateur, Seigneur des armées, brisera la petite bouteille par la terreur; et les plus élevés par la taille seront coupés par le bas, et les grands seront humiliés.
34 Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.
Et les parties épaisses de la forêt seront abattues, et le Liban avec ses hauts cèdres tombera.

< Ishaya 10 >