< Ishaya 10 >

1 Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
Malheur à ceux qui rendent des arrêts iniques, et aux scribes qui écrivent des sentences injustes,
2 don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
écartant du tribunal les faibles, et dépouillant de leur droit les affligés de mon peuple, faisant des veuves leur proie, et pillant les orphelins!
3 Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
Que ferez-vous au jour de la visite, et dans la catastrophe qui viendra de loin? Vers qui fuirez-vous pour avoir du secours, et où déposerez-vous vos trésors?
4 Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Il ne reste qu'à se courber parmi les captifs, ou à tomber parmi les tués. Avec tout cela, sa colère ne s'est point détournée, et sa main reste étendue.
5 “Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
Malheur à Assur, verge de ma colère! Le bâton qui est dans sa main est l'instrument de ma fureur;
6 Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
je l'envoie contre une nation impie, je lui donne mes ordres contre le peuple de mon courroux, pour le mettre au pillage et faire du butin, et le fouler au pied comme la boue des rues.
7 Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
Mais lui, ce n'est pas ainsi qu'il l'entend, et telle n'est pas la pensée de son cœur; car il ne songe qu'à détruire, et à exterminer des nations, non en petit nombre.
8 Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
Il dit: " Mes princes ne sont-ils pas tous des rois?
9 ‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
N'en a-t-il pas été de Calno comme de Carchémis, et de Hamath comme d'Arphad, et de Samarie comme de Damas?
10 Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
Comme ma main a atteint les royaumes des divinités impuissantes, dont les idoles l'emportaient sur celles de Jérusalem et de Samarie; comme j'ai fait à Samarie et à ses dieux,
11 ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
ne ferai-je pas de même à Jérusalem et à ses images? "
12 Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
Mais il arrivera: Quand le Seigneur aura accompli toute son œuvre, sur la montagne de Sion et à Jérusalem: " Je visiterai le fruit du cœur hautain du roi d'Assyrie, et l'arrogance de ses regards altiers. "
13 Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
Car il a dit: " Par la force de ma main j'ai fait cela, et par ma sagesse, car je suis intelligent! J'ai déplacé les bornes des peuples, j'ai pillé leurs trésors, et, comme un héros, j'ai renversé du trône ceux qui y étaient assis.
14 Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
Ma main a saisi, comme un nid, les richesses des peuples, et, comme on ramasse des œufs abandonnés, j'ai ramassé toute la terre, sans que nul ait remué l'aile, ouvert le bec ou poussé un cri! " —
15 Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
La hache se glorifie-t-elle contre la main qui la brandit, la scie s'élève-t'elle contre celui qui la meut? Comme si la verge faisait mouvoir celui qui la lève, comme si le bâton soulevait ce qui n'est pas du bois!
16 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
C'est pourquoi le Seigneur Yahweh des armées, enverra le dépérissement sur ses robustes guerriers, et sous sa magnificence s'embrasera un feu, comme le feu d'un incendie.
17 Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
La lumière d'Israël sera un feu, et son Saint, une flamme, qui consumera et dévorera ses épines et ses ronces, en un seul jour.
18 Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
Et la gloire de sa forêt et de son verger, il l'anéantira de l'âme au corps; ce sera comme un malade qui meurt de consomption.
19 Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
Le reste des arbres de sa forêt pourra être compté; un enfant les inscrirait.
20 A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Et il arrivera en ce jour-là: Le reste d'Israël et les réchappés de la maison de Jacob ne continueront pas de s'appuyer sur celui qui les frappait, mais ils s'appuieront sur Yahweh, le Saint d'Israël, avec fidélité.
21 Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
Un reste reviendra, un reste de Jacob, vers le Dieu fort.
22 Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
Car, quand ton peuple, ô Israël, serait comme le sable de la mer, c'est un reste qui reviendra; la destruction est résolue, elle fera déborder la justice.
23 Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
Car la destruction qu'il a décrétée, le Seigneur Yahweh des armées l'accomplira dans tout le pays.
24 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh des armées: " Ne crains rien d'Assur, ô mon peuple, qui habite Sion, quand il te frappera de la verge, et qu'il lèvera sur toi le bâton, comme autrefois l'Egypte.
25 Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
Car, encore bien peu de temps, et mon courroux cessera, et ma colère se tournera contre eux pour les détruire.
26 Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
Et Yahweh des armées lèvera contre eux le fouet, comme il frappa Madian au rocher d'Oreb, et comme son bâton fut sur la mer; et il le lèvera, comme autrefois en Egypte.
27 A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
Et il arrivera en ce jour-là: Le fardeau d'Assur sera ôté de ton épaule, et son joug de dessus ton cou, et ta vigueur fera éclater le joug.
28 Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
Il est venu à Ajath, il a passé à Magron, il laisse son bagage à Machmas.
29 Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
Ils ont passé le défilé; ils ont campé la nuit à Gaba; Rama est dans l'épouvante; Gabaa de Saül prend la fuite.
30 Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
Pousse des cris de détresse, fille de Gallim! Prête l'oreille, Laïs! Pauvre Anathoth!
31 Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
Medména se disperse, les habitants de Gabim sont en fuite.
32 A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
Encore un jour et il sera à Nobé; il lèvera sa main contre la montagne de la fille de Sion, contre la colline de Jérusalem!...
33 Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
Voici que le Seigneur, Yahweh des armées, abat avec fracas la ramure des arbres; les plus hauts sont coupés, les plus élevés sont jetés par terre.
34 Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.
Les fourrés de la forêt sont taillés avec le fer, et le Liban tombe sous les coups d'un Puissant.

< Ishaya 10 >