< Ishaya 10 >

1 Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
Woe to them that make unrighteous decrees, That write oppressive decisions,
2 don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
To turn away the needy from judgment, And rob the poor of my people of their right; That the widows may become their prey, And that they may plunder the orphans.
3 Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
What will ye do in the day of visitation, And in the desolation which cometh from afar? To whom will ye flee for help, And where will ye leave your glory?
4 Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Forsaken by me, they shall sink down among the prisoners, And fall among the slain. For all this his anger is not turned away, But his hand is stretched out still.
5 “Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
Woe to the Assyrian, the rod of mine anger, The staff in whose hands is the instrument of my indignation!
6 Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
Against an impious nation I will send him, And against a people under my wrath I will give him a charge To gather the spoil, and seize the prey, And to trample them under foot like the mire of the streets.
7 Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
But he doth not so purpose, And his heart doth not so intend; But to destroy is in his heart, And to cut off a multitude of nations.
8 Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
For he saith, “Are not my princes altogether kings?
9 ‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
Is not Calno as Carchemish? Is not Hamath as Arpad? Is not Samaria as Damascus?
10 Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
As my hand hath seized the kingdoms of the idols, Whose graven images were more numerous than those of Jerusalem and Samaria,
11 ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
Behold! as I have done to Samaria and her idols, So will I do to Jerusalem and her images.”
12 Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
But when the Lord hath accomplished his whole work upon Mount Zion and Jerusalem, Then will he punish the fruit of the proud heart of the king of Assyria, And the arrogance of his lofty eyes.
13 Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
For he hath said: “By the strength of my hand I have done it, And by my wisdom; for I am wise; I have removed the bounds of nations, I have plundered their treasures; As a hero have I brought down them that sat upon thrones.
14 Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
The riches of the nations hath my hand seized, as a nest; As one gathereth eggs that have been left, So have I gathered the whole world. And there was none that moved the wing, Or that opened the beak, or that chirped.”
15 Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
Shall the axe boast itself against him that heweth with it? Or shall the saw magnify itself against him that moveth it? As if the rod should wield him that lifteth it! As if the staff should lift up him that is not wood!
16 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
Wherefore the Lord, the Lord of hosts, shall send upon his fat ones leanness, And under his glory shall he kindle a burning, like the burning of a fire.
17 Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
The light of Israel shall be a fire, And his Holy One a flame, Which shall burn and devour his thorns and briers in one day.
18 Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
The glory of his forest and of his fruitful field From the spirit even to the flesh shall he consume; It shall be with them as when a sick man fainteth.
19 Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
The remaining trees of the forest shall be few, So that a child may write them down.
20 A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
In that day shall the remnant of Israel, and they that have escaped of the house of Jacob, no more lean upon him that smote them; They shall lean upon Jehovah, the Holy One of Israel, in truth.
21 Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
The remnant shall return, the remnant of Jacob, to the mighty Potentate;
22 Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
For though thy people, O Israel, be as the sand of the sea, Only a remnant of them shall return. The devastation is decreed; It shall overflow with righteousness.
23 Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
For devastation and punishment doth the Lord, Jehovah of hosts, execute in the midst of the whole land,
24 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
Yet thus saith the Lord, Jehovah of hosts: Fear not, O my people, that dwellest in Zion, because of the Assyrian! With his rod indeed shall he smite thee, And lift up his staff against thee in the manner of Egypt;
25 Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
But yet a very little while, and my indignation shall have past, And my anger shall destroy them.
26 Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
Jehovah of hosts shall raise up against him a scourge, As he smote Midian at the rock of Horeb, And as he lifted up the rod against the sea; Yea, he shall lift it up, as in Egypt.
27 A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
In that day shall his burden be removed from thy shoulder, And his yoke from thy neck; Yea, thy yoke shall be broken, as that of a fat steer.
28 Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
He is come to Aiath; he passeth through Migron; In Michmash he leaveth his baggage;
29 Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
They pass the strait; At Geba they make their night-quarters; Ramah trembleth; Gibeah of Saul fleeth.
30 Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
Cry aloud, O daughter of Gallim! Hear, O Laish! Alas, poor Anathoth!
31 Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
Madmenah hasteth away; The inhabitants of Gebim take to flight.
32 A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
Yet one day shall he rest at Nob, Then shall he shake his hand against the mount of the daughter of Zion, The hill of Jerusalem.
33 Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
But behold! the Lord, Jehovah of hosts, shall lop the branches with fearful force, And the high of stature shall be cut down, And the lofty shall be brought low.
34 Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.
He shall hew the thickets of the forest with iron, And Lebanon shall fall by a mighty hand.

< Ishaya 10 >