< Ishaya 10 >
1 Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
Woe vnto them that decree wicked decrees, and write grieuous things,
2 don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
To keepe backe ye poore from iudgement, and to take away the iudgement of the poore of my people, that widowes may be their pray, and that they may spoyle the fatherlesse.
3 Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
What will ye doe nowe in the day of visitation, and of destruction, which shall come from farre? to whom will ye flee for helpe? and where will ye leaue your glorie?
4 Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Without me euery one shall fall among them that are bound, and they shall fall downe among the slayne: yet for all this his wrath is not turned away, but his hand is stretched out still.
5 “Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
O Asshur, the rodde of my wrath: and the staffe in their hands is mine indignation.
6 Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
I will sende him to a dissembling nation, and I will giue him a charge against the people of my wrath to take the spoyle and to take the pray, and to treade them vnder feete like the mire in the streete.
7 Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
But he thinketh not so, neither doeth his heart esteeme it so: but he imagineth to destroy and to cut off not a fewe nations.
8 Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
For he sayeth, Are not my princes altogether Kings?
9 ‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
Is not Calno as Carchemish? Is not Hamath like Arpad? Is not Samaria as Damascus?
10 Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
Like as mine hand hath founde the kingdomes of the idoles, seeing their idoles were aboue Ierusalem, and aboue Samaria:
11 ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
Shall not I, as I haue done to Samaria, and to the idoles thereof, so doe to Ierusalem and to the idoles thereof?
12 Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
But when the Lord hath accomplished all his worke vpon mount Zion and Ierusalem, I will visite the fruite of the proude heart of the King of Asshur, and his glorious and proud lookes,
13 Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
Because he said, By ye power of mine owne hand haue I done it, and by my wisdome, because I am wise: therefore I haue remooued the borders of the people, and haue spoyled their treasures, and haue pulled downe the inhabitants like a valiant man.
14 Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
And mine hand hath found as a nest the riches of the people, and as one gathereth egges that are left, so haue I gathered all the earth: and there was none to mooue the wing or to open the mouth, or to whisper.
15 Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
Shall the axe boast it selfe against him that heweth therewith? or shall the sawe exalt it selfe against him that moueth it? as if the rod shoulde lift vp it selfe against him that taketh it vp, or the staffe should exalt it selfe, as it were no wood.
16 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
Therefore shall the Lord God of hostes send amog his fat men, leannes, and vnder his glorie he shall kindle a burning, like the burning of fire.
17 Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
And the light of Israel shalbe as a fire, and the Holy one thereof as a flame, and it shall burne, and deuoure his thornes and his briers in one day:
18 Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
And shall consume the glory of his forest, and of his fruitfull fieldes both soule and flesh: and he shalbe as ye fainting of a standard bearer.
19 Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
And the rest of the trees of his forest shalbe fewe, that a childe may tell them.
20 A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
And at that day shall the remnant of Israel, and such as are escaped of the house of Iaakob, stay no more vpon him that smote them, but shall stay vpon ye Lord, ye Holy one of Israel in trueth.
21 Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
The remnant shall returne, euen the remnant of Iaakob vnto the mightie God.
22 Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
For though thy people, O Israel, be as the sand of the sea, yet shall the remnant of them returne. The consumption decreed shall ouerflow with righteousnesse.
23 Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
For the Lord God of hostes shall make the consumption, euen determined, in the middes of all the land.
24 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
Therefore thus saith ye Lord God of hostes, O my people, that dwellest in Zion, be not afraid of Asshur: he shall smite thee with a rod, and shall lift vp his staffe against thee after the maner of Egypt:
25 Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
But yet a very litle time, and the wrath shall be consumed, and mine anger in their destruction.
26 Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
And ye Lord of hostes shall raise vp a scourge for him, according to the plague of Midian in the rocke Oreb: and as his staffe was vpon the Sea, so he will lift it vp after the maner of Egypt.
27 A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
And at that day shall his burden be taken away from off thy shoulder, and his yoke from off thy necke: and the yoke shalbe destroied because of the anoynting.
28 Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
He is come to Aiath: he is passed into Migron: at Michmash shall he lay vp his armour.
29 Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
They haue gone ouer the foorde: they lodged in the lodging at Geba: Ramah is afraide: Gibeah of Saul is fled away.
30 Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
Lift vp thy voyce, O daughter Gallim, cause Laish to heare, O poore Anathoth.
31 Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
Madmenah is remoued: the inhabitants of Gebim haue gathered themselues together.
32 A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
Yet there is a time that he will stay at Nob: he shall lift vp his hand towarde the mount of the daughter Zion, the hill of Ierusalem.
33 Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
Beholde, the Lord God of hostes shall cut off the bough with feare, and they of high stature shalbe cut off, and the hie shalbe humbled.
34 Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.
And he shall cut away the thicke places of the forest with yron, and Lebanon shall haue a mightie fall.