< Ishaya 10 >

1 Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
禍哉,那些制定不義的法例,記錄不義的斷案,
2 don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
為屈枉小民的案件,剝削我窮民的權利,攘奪寡婦和劫掠孤兒的人!
3 Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
當懲罰之日,風暴由遠而近的時候,你們將怎樣應付﹖你們將向誰求助﹖你們的財寶將棄於何地﹖
4 Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
唯有屈伏在被俘者中,倒斃在被殺者下;然而他的震怒並未因此而熄滅,他的手仍然伸著。
5 “Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
禍哉,亞述!我義怒的木棒,我震怒的棍杖!
6 Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
我派遣她是為攻擊一個邪惡的百姓,我委任他是為攻擊我所憤恨的民族,為擄掠劫奪,並為蹂躪他們,有如街上的糞土。
7 Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
但她並沒有這樣想,心裏也沒有這樣推測,只圖肆意破壞,剿滅不少的民族。
8 Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
因為她說:「我的首領不都是君王嗎﹖
9 ‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
加耳諾不是與與加革米士一樣嗎﹖哈瑪特不是與阿爾帕得一樣嗎﹖撒瑪黎雅不是與大馬士革一樣嗎﹖
10 Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
我的手既然征服了這些偶像的王國--況且他們的偶像還多過耶路撒冷和撒瑪黎雅--
11 ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
難道我不能對待耶路撒冷和她的神像,有如對待了撒瑪黎雅和她的偶像嗎﹖」
12 Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
當吾主對熙雍山和耶路撒冷完成了他的一切工作時,必要懲罰亞述王心高氣傲的功績,和他目空一切的驕傲。
13 Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
因為他曾說過:「我完成了這一切,全憑我的手和我的智慧,因為我是聰明的;我撤除了各民族的界限,擄掠了他們的財寶,有如強者打倒了居於高位的人。
14 Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
我的手奪取了列國的財富,有如取諸窩巢;我兼併了大地,有如拾取遺卵,沒有誰敢鼓翼和張口鼓噪。」
15 Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
斧頭豈能對用斧頭砍伐的人自豪﹖鋸豈能向拉鋸的人自誇﹖難道棍杖能揮動那舉它的人﹖木棒能舉起那不是木頭的人﹖
16 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
因此吾主,萬軍的天主,將瘦弱放在她的肥碩之中,在她的光輝之下燃起火燄,有如烈火焚燒。
17 Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
以色列的光將變為火,他的聖者將變為烈燄,一日間即將她的荊棘蒺藜焚燬。
18 Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
她的叢林和她田園的華麗,必將由內到外毀滅,有如為蟲蝕盡一樣。
19 Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
她的叢林所剩餘的樹木不多,一個兒童就能計算。
20 A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
到那一日,以色列的遺民和雅各伯家的逃亡者,不再依恃打擊他們的人,卻誠心依賴上主,以色列的聖者。
21 Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
遺民必將歸回,雅各伯的遺民必將歸依強有力的天主!
22 Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
以色列啊! 你的百姓雖然多如海沙,其中唯有殘存者得以歸回:毀滅已經決定,但是充溢著公義,
23 Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
因為吾主,萬軍的上主必在大地上執行所決定的毀滅。
24 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
因此吾主,萬軍的上主這樣說:我的百姓,熙雍的居民!亞述雖然用木棒痛擊你,像埃及一樣,舉起棍杖敲打你,但你不必害怕,
25 Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
因為瞬息間我的怒氣即將終止,我的憤怒將轉為他們的毀滅。
26 Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
萬軍的上主將揮動刑鞭鞭打他們,有如昔日在曷勒布磐石處打擊米德楊一樣;高舉向海上伸出的棍杖,有如在埃及一樣。
27 A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
到那日,她的重負將由你肩上卸下,她的重軛將由你頸上解除。
28 Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
破壞者由黎孟而來,來到阿雅特,經過米革龍,將輜重貯在米革瑪斯;
29 Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
又穿過要隘,夜宿革巴。辣瑪驚慌了,撒烏耳的基貝亞逃走了。
30 Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
巴特加林!你們應大聲疾呼;拉依士!你們應該傾聽;阿納托特!你們應該回答。
31 Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
瑪德默納走散了,革平的居民逃避了。
32 A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
在諾布暫停一天,遂即揮手指向熙雍女兒山,耶路撒冷的山崗。
33 Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
看啊!吾主,萬軍的上主將用斧鉞砍伐枝幹:高出的要削去,聳出的要砍低。
34 Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.
他將用鐵斧砍伐叢林,黎巴嫩和她的壯麗必被伐倒。

< Ishaya 10 >